Mazauna Djibo a Burkina Faso sun buƙaci cikakkiyar kariya daga ƴan ta’adda

Mazauna garin Djibo na lardin Soum a Burkina Faso sun gudanar da zanga-zanga a ranar Lahadi don neman a inganta musu tsaro biyo bayan mummunan harin ta’adanci da aka kai garin.

Mata, maza da yara ne suka  bazama kan titunan garin  a matsayin martani ga kutsen da ƴan bindiga suka yi a gari  amakon da ya gabata, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutane 3, waɗanda ƴan ta’addan suka yi wa yankan rago.

Ɗaya  daga cikin masu zanga-zangar da ya bayyana dalilin fitowar su cikin  fushi ta cikin wani hoton bidiyo, ya ce ƴan ta’addan su na yi musu kutse cikin birnin, inda su ke kashe iyaye, matansu da ƴaƴansu.

Dubban mutane ne suka arce daga wasu sassan birnin da ɗan kayayyakin da za su iya ɗibawa, biyo bayan wa’adin da  wata ƙungiyar ƴan ta’adda ta ɗibar musu.

Hotunan da aka wallafa a shafukan dandalin sada zumunta sun nuna ɗimbim mutane a ruɗe su na barin birnin a ƙasa da jakuna.

Wasu mazauna birnin sun ce ƙungiyar ƴan ta’addan ta bai wa al’ummar  su koma yankuna  na 7,8 da 9 na Djibo. Amma waɗannan yankuna sun kasance a ƙarƙashin ikonsu tsawon shekara guda, amma a maimakon haka sai su ka nufi sansanin soji kai tsaye a cewar majiyoyi da dama.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 7 hours 9 minutes 16 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 8 hours 50 minutes 41 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com