Home General Mazauna Djibo a Burkina Faso sun buƙaci cikakkiyar kariya daga ƴan ta’adda

Mazauna Djibo a Burkina Faso sun buƙaci cikakkiyar kariya daga ƴan ta’adda

Mazauna garin Djibo na lardin Soum a Burkina Faso sun gudanar da zanga-zanga a ranar Lahadi don neman a inganta musu tsaro biyo bayan mummunan harin ta’adanci da aka kai garin.

Mata, maza da yara ne suka  bazama kan titunan garin  a matsayin martani ga kutsen da ƴan bindiga suka yi a gari  amakon da ya gabata, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutane 3, waɗanda ƴan ta’addan suka yi wa yankan rago.

Ɗaya  daga cikin masu zanga-zangar da ya bayyana dalilin fitowar su cikin  fushi ta cikin wani hoton bidiyo, ya ce ƴan ta’addan su na yi musu kutse cikin birnin, inda su ke kashe iyaye, matansu da ƴaƴansu.

Dubban mutane ne suka arce daga wasu sassan birnin da ɗan kayayyakin da za su iya ɗibawa, biyo bayan wa’adin da  wata ƙungiyar ƴan ta’adda ta ɗibar musu.

Hotunan da aka wallafa a shafukan dandalin sada zumunta sun nuna ɗimbim mutane a ruɗe su na barin birnin a ƙasa da jakuna.

Wasu mazauna birnin sun ce ƙungiyar ƴan ta’addan ta bai wa al’ummar  su koma yankuna  na 7,8 da 9 na Djibo. Amma waɗannan yankuna sun kasance a ƙarƙashin ikonsu tsawon shekara guda, amma a maimakon haka sai su ka nufi sansanin soji kai tsaye a cewar majiyoyi da dama.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp