Home General Sojojin Najeriya sun kama masu safarar bindigogi biyar a Filato

Sojojin Najeriya sun kama masu safarar bindigogi biyar a Filato

Dakarun sojin Najeriya sun ce sun kama mutum biyar waɗanda suka shahara wajen safarar bindigogi a jihar Filato tare kuma da ƙwato makamai.

Wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na sojojin Manjo Stephen Zhakom ya fitar ranar Talata, ya ce an samu nasarar ce bayan wani aikin samame da suka kai jihar, inda ya ce hakan na cikin zimmar sojoji na ganin sun kakkaɓe masu rike da makamai ba bisa ka’ida ba.

“An fara samamen da dakarun Operation Safe Haven suka yi tare da haɗin gwiwar wasu jami’an tsaro ne a ranar Litinin da daddare har zuwa safiyar yau Talata,” in ji shi.

Ya ce dakarun sun yi wa maɓoyar wani mai safarar bindigogi mai suna Mohammed Sani a garin Naraguta kan hanyar Bauchi zuwa Jos, inda nan ne kuma suka yi nasarar kama shi tare da wasu mutum huɗu.

Makamai da sojojin suka kwace sun haɗa da bindigar AK-47 guda biyu, alburusai da sauransu.

Zhakom ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike kan mutanen da aka kama d anufin ƙara samun bayanai da za su kai ga kama sauran masu harkar domin daƙile aikinsu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp