Home General Sojojin Najeriya sun kama masu safarar bindigogi biyar a Filato

Sojojin Najeriya sun kama masu safarar bindigogi biyar a Filato

Dakarun sojin Najeriya sun ce sun kama mutum biyar waɗanda suka shahara wajen safarar bindigogi a jihar Filato tare kuma da ƙwato makamai.

Wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na sojojin Manjo Stephen Zhakom ya fitar ranar Talata, ya ce an samu nasarar ce bayan wani aikin samame da suka kai jihar, inda ya ce hakan na cikin zimmar sojoji na ganin sun kakkaɓe masu rike da makamai ba bisa ka’ida ba.

“An fara samamen da dakarun Operation Safe Haven suka yi tare da haɗin gwiwar wasu jami’an tsaro ne a ranar Litinin da daddare har zuwa safiyar yau Talata,” in ji shi.

Ya ce dakarun sun yi wa maɓoyar wani mai safarar bindigogi mai suna Mohammed Sani a garin Naraguta kan hanyar Bauchi zuwa Jos, inda nan ne kuma suka yi nasarar kama shi tare da wasu mutum huɗu.

Makamai da sojojin suka kwace sun haɗa da bindigar AK-47 guda biyu, alburusai da sauransu.

Zhakom ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike kan mutanen da aka kama d anufin ƙara samun bayanai da za su kai ga kama sauran masu harkar domin daƙile aikinsu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp