Mutum sama da miliyan biyu ne suka karɓi katin zaɓe a Edo – INEC

Hukumar zabe a Najeriya INEC ta sanar da cewa sama da mutum miliyan biyu ne suka karbi katin zaɓensu na dindindin gabanin zaɓen gwamnan jihar Edo da ke tafe ranar Asabar.

Wata sanarwa da hukumar ta fitar a shafinta na X, ta ce mutum 2,629,025 suka yanki katin zaɓe a faɗin jihar.

“An karɓi katuna 2,249,780 yayin da 379,245 sune suka rage ba a karɓa ba zuwa ranar Litinin 16 ga watan Satumban 2024 bayan ƙara wa’adi da muka yi,” in ji INEC.

Hakan ya nuna cewa an karɓi kashi 85.57 na katunan zaɓe a jihar, a cewar hukumar.

Za a gudanar da zaɓen a ɗaukacin rumfunan zaɓe 4,519 da ke faɗin jihar.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 8 hours 57 minutes 7 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 38 minutes 32 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com