Home General EFCC ta ce har yanzu tana neman Yahaya Bello ruwa a jallo

EFCC ta ce har yanzu tana neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Tababa da rashin tabbas sun mamaye ziyarar hukumar EFCC da tsohon gwamnan Kogi Yahaya Bello yace ya yi domin amsa tambayoyi dangane da zarge zargen da ake masa na rub da ciki da kudaden talakawa da kuma halarta kudaden haramun.

Yayin da tsohon gwamnan ta hannun mai magana da yawunsa Ohiare Michael ya ce yau ya kai kansa EFCC tare da rakiyar lauyoyinsa da kuma gwamnan Kogi Usman Ododo, Hukumar EFCC ta fitar da sanarwar watsi da ikrarin da kuma bayyana cewar har yanzu ta na neman shi ruwa a jallo.

Bello ya shaida wa manema labarai cewar bayan ziyarar domin amsa tambayoyi EFCC ta ce masa ya tafi gida ba tare da masa tambayoyi akan zargin karkata kudaden da suka kai naira biliyan 80 ba.

Tsohon gwamnan ya bukaci hukumar yaki da cin hancin ta ci gaba da aiki da dokokin da suka samar da ita tare da mutunta ‘yancin jama’ar kasa, ya yin da ya kara da cewar matakan da ya dauka na kin amsa gayyatar hukumar ya yi su ne domin kare hakkokinsa.

Sai dai mai magana da yawun EFCCn Dele Oyewale ya ce babu gaskiya dangane da mika wuyar tsohon gwamnan, kuma har yanzu suna neman sa ruwa a jallo.

Ko da yake a safiyar Alhamis, jami’an hukumar dake yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa ta’annati na EFCC sun zagayi gidan da ake zargin Yahaya Bello na ciki, wanda suke bukatar ya mika kansa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp