Home General EFCC ta ce har yanzu tana neman Yahaya Bello ruwa a jallo

EFCC ta ce har yanzu tana neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Tababa da rashin tabbas sun mamaye ziyarar hukumar EFCC da tsohon gwamnan Kogi Yahaya Bello yace ya yi domin amsa tambayoyi dangane da zarge zargen da ake masa na rub da ciki da kudaden talakawa da kuma halarta kudaden haramun.

Yayin da tsohon gwamnan ta hannun mai magana da yawunsa Ohiare Michael ya ce yau ya kai kansa EFCC tare da rakiyar lauyoyinsa da kuma gwamnan Kogi Usman Ododo, Hukumar EFCC ta fitar da sanarwar watsi da ikrarin da kuma bayyana cewar har yanzu ta na neman shi ruwa a jallo.

Bello ya shaida wa manema labarai cewar bayan ziyarar domin amsa tambayoyi EFCC ta ce masa ya tafi gida ba tare da masa tambayoyi akan zargin karkata kudaden da suka kai naira biliyan 80 ba.

Tsohon gwamnan ya bukaci hukumar yaki da cin hancin ta ci gaba da aiki da dokokin da suka samar da ita tare da mutunta ‘yancin jama’ar kasa, ya yin da ya kara da cewar matakan da ya dauka na kin amsa gayyatar hukumar ya yi su ne domin kare hakkokinsa.

Sai dai mai magana da yawun EFCCn Dele Oyewale ya ce babu gaskiya dangane da mika wuyar tsohon gwamnan, kuma har yanzu suna neman sa ruwa a jallo.

Ko da yake a safiyar Alhamis, jami’an hukumar dake yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa ta’annati na EFCC sun zagayi gidan da ake zargin Yahaya Bello na ciki, wanda suke bukatar ya mika kansa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp