Ambaliya: Gwamnatin Najeriya za ta gina madatsan ruwa biyar domin tare ruwan dam ɗin Lagdo

Gwamnatin Najeriya ta bakin Hukumar Ruwa ta Najeriya wato Nigeria Hydrological Services Agency (NIHSA) ta ce za ta gina wasu madatsun ruwa biyar domin kare ambaliyar da ke faruwa a sanadiyar ruwan da ke mamal daga dam ɗin Lagbo na Kamaru.

Darakta-Janar na NIHSA, Umar Mohammed ne ya bayyana hakan a zantawarsa ta talabijin na Channels a ranar Alhamis.

Hukumar ta gargaɗi ƴan Najeriya da suke zaune a wuraren da ake ambaliya su canja mazauni saboda sako ruwan da aka yi daga Kamaru.

Jihohin da ake fargabar dam ɗin na Kamaru zai jawo ambaliya sun haɗa da Adamawa da Taraba da Benue da Nasarawa da Kogi da Edo da Delta da Anambra da Bayelsa da Kuros Riba da Rivers.

Mohammed, wanda daraktan aikace-aikace na hukumar Femi Bejide ya wakilta, ya ce hukumar ta miƙa wa Fadar Shugaban Ƙasa rahoto, inda a ciki ta bayyana hanyoyin da za a kiyaye aukuwar ambaliyar, ciki har da sauya wuraren da wasu dam suke.

“Sannan mun miƙa buƙatar gina wasu dam guda biyar domin tare ruwan dam ɗin Lagdo,” in ji shi.

“Amma dole za a canja inda wasu dam suke, sannan a faɗaɗa gaɓar tekunan Neja da Benuwe.”

Sako ruwan dam ɗin Lagdo ya zo ne kwanaki kaɗan bayan dam ɗin Alau a Maiduguri ya yi ambaliya, inda aƙalla mutum 30 suka mutu, sannan ya raba dubbai da muhallansu.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1191 days 2 hours 23 minutes 18 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1173 days 4 hours 4 minutes 43 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com