Home General Ambaliya: Gwamnatin Najeriya za ta gina madatsan ruwa biyar domin tare ruwan...

Ambaliya: Gwamnatin Najeriya za ta gina madatsan ruwa biyar domin tare ruwan dam ɗin Lagdo

Gwamnatin Najeriya ta bakin Hukumar Ruwa ta Najeriya wato Nigeria Hydrological Services Agency (NIHSA) ta ce za ta gina wasu madatsun ruwa biyar domin kare ambaliyar da ke faruwa a sanadiyar ruwan da ke mamal daga dam ɗin Lagbo na Kamaru.

Darakta-Janar na NIHSA, Umar Mohammed ne ya bayyana hakan a zantawarsa ta talabijin na Channels a ranar Alhamis.

Hukumar ta gargaɗi ƴan Najeriya da suke zaune a wuraren da ake ambaliya su canja mazauni saboda sako ruwan da aka yi daga Kamaru.

Jihohin da ake fargabar dam ɗin na Kamaru zai jawo ambaliya sun haɗa da Adamawa da Taraba da Benue da Nasarawa da Kogi da Edo da Delta da Anambra da Bayelsa da Kuros Riba da Rivers.

Mohammed, wanda daraktan aikace-aikace na hukumar Femi Bejide ya wakilta, ya ce hukumar ta miƙa wa Fadar Shugaban Ƙasa rahoto, inda a ciki ta bayyana hanyoyin da za a kiyaye aukuwar ambaliyar, ciki har da sauya wuraren da wasu dam suke.

“Sannan mun miƙa buƙatar gina wasu dam guda biyar domin tare ruwan dam ɗin Lagdo,” in ji shi.

“Amma dole za a canja inda wasu dam suke, sannan a faɗaɗa gaɓar tekunan Neja da Benuwe.”

Sako ruwan dam ɗin Lagdo ya zo ne kwanaki kaɗan bayan dam ɗin Alau a Maiduguri ya yi ambaliya, inda aƙalla mutum 30 suka mutu, sannan ya raba dubbai da muhallansu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp