Home General Dalilin da yasa gwamnatin Kano ta rushe Jami’ar ilimi ta Sa’adatu

Dalilin da yasa gwamnatin Kano ta rushe Jami’ar ilimi ta Sa’adatu

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya soke Jami’ar Ilimi ta Sa’adatu Rimi da ke Kumbotso, ya mayar da ita kwalejin ilimi.

Kwamishinan yada labarai na Jihar Kano, Baba Ɗantiye, ya sanar cewa, “Gwamna ya rushe hukumar gudanarwar jami’ar nan take”, ya mayar da ita tsohon matsayinta na Kwalejin Ilimi na Sa’adatu Rimi.

“Ya umarci shugaban rusasshiyar jami’ar da ya mika ragamar jagoranci ga mataimakinsa mafi girman matsayi, daga bisani gwamantin jihar za ta sanar da mataki na gaba.”
a bayyana cewar an ɗauki matakin ne bayan samun rahoton kwamitin da gwamnatin ta kafa domin lalubo hanyoyin bunkasa harkokin ilimi da kuma tattaunawa da ƙwararru da sauran masu ruwa da tsaki.

A cewarsa, an gano cewa tun da farko akwai illa a ɗaga darajar Kwalejin Ilimi na Sa’adatu Rimi zuwa jami’a, la’akari da “kasancewarta a mashigar garin Kano inda dalibai da dama daga wajen birnin suke karatu.

“Hakan na haifar da barazanar rasa ƙwarrarrun malamai, bambancin albashi da kuma matsalolin gudanar da ita cikin inganci.

“Sannan Majalisar Zartarwa ta lura cewa jihohi da dama a faɗin Najeriya sun ci gaba da gudanar da kwalejojin iliminsu ba tare da wata matsala ba, ƙarƙashin tsarin bayar da takardun shaidar kwarewar malanta da kuma shaidar digiri, ba tare da kwalejojin sun koma jami’o’i ba.”

A cewarsa, soke matsayin jami’ar “ba zai shafi karatun ɗalibanta ba, kuma kwalejin za ta kasance mai bayar da shaidar kammala karatun digiri.

“Sannan za ta ci gaba da gudanar da darussa a wasu fannonin,” da ba na ilimi ba.

Ana iya tuna cewa tsohuwar gwamnatin Abdullahi Ganduje ce ta daga darajar kwalejin ilimin na Sa’adatu Rimi mallakar gwamnatin jihar zuwa jami’ar ilmi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp