Home General Dalilin da yasa gwamnatin Kano ta rushe Jami’ar ilimi ta Sa’adatu

Dalilin da yasa gwamnatin Kano ta rushe Jami’ar ilimi ta Sa’adatu

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya soke Jami’ar Ilimi ta Sa’adatu Rimi da ke Kumbotso, ya mayar da ita kwalejin ilimi.

Kwamishinan yada labarai na Jihar Kano, Baba Ɗantiye, ya sanar cewa, “Gwamna ya rushe hukumar gudanarwar jami’ar nan take”, ya mayar da ita tsohon matsayinta na Kwalejin Ilimi na Sa’adatu Rimi.

“Ya umarci shugaban rusasshiyar jami’ar da ya mika ragamar jagoranci ga mataimakinsa mafi girman matsayi, daga bisani gwamantin jihar za ta sanar da mataki na gaba.”
a bayyana cewar an ɗauki matakin ne bayan samun rahoton kwamitin da gwamnatin ta kafa domin lalubo hanyoyin bunkasa harkokin ilimi da kuma tattaunawa da ƙwararru da sauran masu ruwa da tsaki.

A cewarsa, an gano cewa tun da farko akwai illa a ɗaga darajar Kwalejin Ilimi na Sa’adatu Rimi zuwa jami’a, la’akari da “kasancewarta a mashigar garin Kano inda dalibai da dama daga wajen birnin suke karatu.

“Hakan na haifar da barazanar rasa ƙwarrarrun malamai, bambancin albashi da kuma matsalolin gudanar da ita cikin inganci.

“Sannan Majalisar Zartarwa ta lura cewa jihohi da dama a faɗin Najeriya sun ci gaba da gudanar da kwalejojin iliminsu ba tare da wata matsala ba, ƙarƙashin tsarin bayar da takardun shaidar kwarewar malanta da kuma shaidar digiri, ba tare da kwalejojin sun koma jami’o’i ba.”

A cewarsa, soke matsayin jami’ar “ba zai shafi karatun ɗalibanta ba, kuma kwalejin za ta kasance mai bayar da shaidar kammala karatun digiri.

“Sannan za ta ci gaba da gudanar da darussa a wasu fannonin,” da ba na ilimi ba.

Ana iya tuna cewa tsohuwar gwamnatin Abdullahi Ganduje ce ta daga darajar kwalejin ilimin na Sa’adatu Rimi mallakar gwamnatin jihar zuwa jami’ar ilmi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp