Home General Ambaliyar Maiduguri: Zulum ya kafa kwamitin rabon tallafi

Ambaliyar Maiduguri: Zulum ya kafa kwamitin rabon tallafi

Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya kafa kwamitin rabon kayan tallafi ga mutanen da iftila’in ambliya ya shafa a Maiduguri, babban birnin jihar.

Wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar Bukar Tijjani ya fitar, gwamna Zulum ya ce kwamitin mai mamboi 35 zai kunshi wakilai daga hukumomi da dama da suka haɗa da hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC da takwararta ta ICPC da kuma hukumar tsaro ta farin kaya wato DSS.

Sauran mambobin kwamitin sun haɗa masu ba shi shawara da wakilan hukumar raya yankin arewa maso gabas (NEDC), ma’aikatar wasanni da ci gaban matasa da ma’aikatar kudi da ta mata da kuma hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar (SEMA) da sauransu.

Gwamna Zulum ya buƙaci mambobin kwamitin da su jajirce wajen sauke nauyin da aka ba su da kuma yin gaskiya.

“Za mu tabbatar da cewa an yi amfani da kuɗin ta hanyar da ya dace, za mu tsaya mu ga tallafin ya kai ga mutanen da aka yi domin su,” in ji Zulum.

Ya ce gwamnatin jihar za ta tabbatar da ganin an sake gyara wurare kamar asibitoci da hanyoyi da kuma gadoji.

Mutane da dama dai, musamman masu hannu da shuni suka bayar da tallafin kuɗaɗe da kuma kayan abinci zuwa ga waɗanda ambaliyar Maiduguri ta shafa.

Ya ce sun samu karɓar tallafi da ya kai naira biliyan 4.4 zuwa cikin asusun tallafin jihar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp