Home General An kashe fitattun ƴanbindiga Kachalla Sani Black da Sharme

An kashe fitattun ƴanbindiga Kachalla Sani Black da Sharme

Afghan military personnel walk near the airport during fighting between Taliban militants and Afghan security forces in Kunduz on October 1, 2015. Afghan forces pushed into the centre of Kunduz on October 1, triggering pitched gunfights as they sought to flush out Taliban insurgents who held the northern city for three days in a stinging blow to the country's NATO-trained military The stunning fall of the provincial capital, even temporarily, highlighted the stubborn insurgency's potential to expand beyond its rural strongholds in the south of the country Afghan forces, hindered by the slow arrival of reinforcements but backed by NATO special forces and US air support, struggled to regain control of the city after three days of heavy fighting. AFP PHOTO / Wakil Kohsar

Rahotanni na nuna cewa an kashe ƙasurgumin ɗanbindiga, Kachalla Sani Black a Zamfara.

Ƴan sa-kai ne suka fafata da ɗanbindigar, suka kashe shi, suka ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda biyu, da wasu ƙudade.

Kafar PRNigeria ta ruwaito cewa bayan kashe ɗanbindigar, an kuma kashe ƴaƴansa biyu a fafatawar da aka yi a yankin Magama Mai Rake da ke ƙaramar hukumar Maru da ke jihar Zamfara.

Kachalla Sani Black fitaccen ɗanbindiga ne da ya addabi yankin Chabi da Ɗan Sadau a ƙaramar hukumar Maru da wasu yankuna na arewacin Zamfara da Kaduna da Neja da Kebbi.

Rahotanni sun ce yana da daba mai yawa da suka haura 150, sannan kuma a dabarsa a kan samu labarin yi wa mata fyade bayan an yi garkuwa da su.

A wani labarin kuma, rikicin cikin gida ya ci wani fitaccen ɗanbindigar mai suna Kachalla Tukur Sharme a Kaduna.

Sharme ya mutu ne a sanadiyar rigimar da ta ɓarke a tsakanin dabarsa da wata dabar a wani waje da ake kira ‘Hambakko’ da ke tsakanin dajin Rijana da dajin Kaso, wadda ta yi sanadiyar tserewar wasu wadanda aka yi garkuwa da su.

A wata sanarwa da Kwamishinan Harkokin Cikin Gida na Kaduna Samuel Aruwan ya fitar, ya ce Sharme na ya jagoranci sace ɗaliban makarantar Bethel Baptist High School da ke Kaduna su 121.

Sharme ya daɗe yana addabar yankin Rijana da Kasarami da Jaka da-Rabi da Millenium City da Maraban Rido da Kujama da sauran garuruwan Jihar Kaduna.

Sanarwat ta ƙara da cewa wasu ƴanbindigar sun ji rauni a fafatawar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp