Home General EFCC ta kama tsohon gwamnan Taraba kan badakalar Biliyan 27

EFCC ta kama tsohon gwamnan Taraba kan badakalar Biliyan 27

Hukumar dake yaki da masu yiwa tattalin arzikin Nijeriya zagon kasa ta EFCC ta tsare tsohon Gwamnan jihar Taraba Darius Ishaku bisa zargin halasta kudin haram ya zuka kai naira biliyan 27 a lokacin da yake bisa karagar mulkin jihar

EFCC ta na tuhuwar tsohon Gwamnan  wasu tuhume-tuhume guda goma sha biyar dake da nasaba da almundahana da dukiyar al’umma

Rahotanni sun bayyana cewa, a wannan Juma’a ne jami’an EFCC suka yi dirar mikiya a gidan tsohon gwamnan da ke Abuja wanda wa’adinsa ya ƙare a shekarar 2023 bayan shafe tsawon shekaru takwas a kan madafun iko.

EFCC ta ce gwamnan yana hannun hukumar inda ake titsiye shi.

Hukumar ta EFCC ta kammala tattara aƙalla tuhume-tuhume 15 da ake zargin tsohon gwamnan kuma nan ba da jimawa ba zai gurfana a gaban kuliya.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp