Home General Najeriya ta fara sayar da ɗanyen mai da kuɗin naira

Najeriya ta fara sayar da ɗanyen mai da kuɗin naira

Old Naira

Gwamnatin Najeriya ta ce ƙasar ta fara sayar da ɗanyen mai da tataccen mai da kuɗin ƙasar wato naira.

Ministan kuɗi da tattalin arzikin na ƙasar, Wale Edun ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ma’aikatar kuɗin ƙasar, ta wallafa a shafinta na X ranar Asabar.

Sanarwar ta ce an fara sayar da ɗanyen man da kuɗin naira ne tun daga ranar ɗaya ga watan Okotoban da muke ciki.

Ministan ya ce hakan na daga cikin matakin da gwamnatin Bola Tinubu ta ɗauka da ake sa ran zai haɓa tattalin arzikin ƙasar da ci gaba da zaman lafiya da dogaro da kai.

Mista Edun ya ce Najeriya za ta ci gaba da bin matakan da suka dace, lura da halin da kasuwannin ɗanyen a duniya ke ciki wajen ciyar da ƙasar gaba.

Matakin na zuwa ne mako tara bayan majalisar zartarwar ƙasar ta amince da ƙudurin Shugaba Tinubu na umartar kamfanin NNPCL ta sayar wa matatar mai ta Dangote da sauran matatun cikin gida ɗanyen mai da kuɗin ƙasar wato naira.

Masu sharhi dai naganin matakin sayar da man da naira maimakon dala zai age farashin kuɗin ƙasar waje a ƙasa, lamarin da suke ganin zai karya farashin dala tare da rage hauhawar farashi a ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp