Home AFIRKA Fararen hula 10 sun mutu sakamakon harin ƴan ta’adda a Burkina Faso

Fararen hula 10 sun mutu sakamakon harin ƴan ta’adda a Burkina Faso

Wasu da ake zargi yan ta’adda masu ikirarin jihadi ne sun kashe fararen hula 10 a wata kasuwa da ke arewacin ƙasar ƙarshen makon da ya gabata, kamar yadda jami’an yankin su ka bayyana a ranar Talata.

Wasu mazauna lardin Gnagna inda lamarin ya faru ssun ce ƴan ta’addan sun farmaki garin ne da yammacin Lahadi, inda su ka kashe mutane tare da raunata da dama.

Wani jami’in asibiti a yankin ya ce yana da matuƙar wahala a tantance adadin waɗanda su ka mutu, amma ya ce  akalla mutane 10 sun mutu, kana 50 su ka jikkata.

Ganau sun ce maharan sun sun shiga garin ne kuma su ka fara harbi kan uwa da wabi, inda su ka tarwatsa jama’a, har su ka fara fasa shaguna su na sata.

Ƙasar da ke yankin yammacin nahiyar Afrika tana fama da matsalar ƴan ta’adda masu ikirarin jihadi da su ka kwarara daga makwafciyarta Mali tun daga shekarar 2015.

Dubban fararen hula, sojoji da yan sanda ne aka kashe, lamarin da ya fusata wasu hafsoshin soji har su ka yi juyin mulki  a shekarar 2022.

Sama da mutane dubu 26 ne su ka mutu sakamakon hare-haren ƴan ta’adda a Burkina Faso tun daga shekarar 2015, fiye da dubu 6 daga cikin su a wannan shekarar aka kashe su.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp