Home AFIRKA Hukumomin Libya na ci gaba da tsare ƴan Najeriya da Nijar sama...

Hukumomin Libya na ci gaba da tsare ƴan Najeriya da Nijar sama da 900 – Rahotanni

Wasu rahotanni daga kasar Libiya na cewa, wani bangare na hukumomin kasar, sun kama wasu ƴan kasashen Afrirka bakin haure bakaken fata yawanci ƴan asalin kasar Jumhuriyar Nijar da Najeriya sama da 900.

Sama da wata daya da ake rike da wadannan mutane sai dai har zuwa yanzu babu wani cikaken bayani game da inda suke.

Tuni wasu da suka galabaita daga ciki suka fara mutuwa.

Wani daga wadanda suka tsira a lokacin da aka kai samamen da jami’an tsaro suka kai a lokacin da suka kama ƴan Afirkar ya shaida wa BBC cewe ” Ranar 6 ga watan Satumba ne jami’an tsaron suka kai samame, suka kama mutanen Nijar da Najeriya, ” Nima ina cikin mutanen amman na gudu ne shiyasa ba a kama ni ba, amman sun dauki mutanen da suka kai 500 a lokacin.”

“Daga baya cikin wadanda suka kama din basu anshe amsu wayoyi ba, sune suka kira suke fadin cewa adadin mutanen da aka kama sun kai 900 kuma yawancinsu ƴan Nijar ne” cewar mutumin.

Wasu daga cikin farar hula na Nijar din na ci gaba da kira ga hukumomin ƙasar da su sanya baki kan lamarin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp