Home General Ƴan ta’addar da suka tsere daga Zamfara na yi wa Kano barazana

Ƴan ta’addar da suka tsere daga Zamfara na yi wa Kano barazana

Hukumomi a Najeriya sun tsaurara matakan tsaro da kuma sa-ido sosai a birnin Kano, bayan da wani rahoton da hukumomin tara bayan sirri suka gano cewa yanzu ɗimbin ƴan bindiga sun tsere daga Zamfara inda suke fakewa a cikin birnin wanda shi ne mafi girma a arewacin kasar.

Kamfanin Dillancin Labaran Faransa AFP ne ya sanar da hakan, bayan da ya samo kwafin wasikar da hukumomin tara bayanan sirri daga Zamfara suka tura wa takwarorinsu da ke Kano.

A cewar AFP, tun a ranar Litinin da ta gabata ne aka gabatar wa gwamnan jihar Kano da wannan rahoto, da ke cewa mafi yawan ƴan bindigar tuni suka mallaki gidaje a cikin birnin Kano, yayin da wasu ke fakewa a unguwannin Rijiyar Zaki, Tudun Yola, Ja’en, Ɗorayi Babba, Rijiyar Lemo da kuma Ƴan Awaki.

Bisa ga dukan alamu, rahoton ya ce mafi yawan ƴan bindigar sun nemi mafaka a birnin Kano ne saboda tsanantar hare-hare da jami’an tsaro ke kai musu a cikin ƴan kwanakin nan, yayin da wasu suka mallaki gidajen tsawon shekaru a birnin a daidai lokacin da suke taimaka wa ƴan bindigar da ke gudanar da ayyukan tsagarenci a jihohin Zamfara, Katsina da kuma Kaduna.

Wasu majiyoyi biyu na tsaro, sun tabbatar wa Kamfanin Dillancin Labaran AFP da cewa rahoton ya shiga hannuwansu, yayin da wata majiyar ke cewa yanzu tana aiki tukuru domin zaƙulo su a cikin gaggawa.

To sai dai majiyar na cewa yanzu haka jami’an tsaro na aiki ne a asirce domin ka da jama’a su shiga hali na firgita.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp