Home Labarai Hukumar NIS na shirin kafa shingen bincike a mashigar jihar Kano

Hukumar NIS na shirin kafa shingen bincike a mashigar jihar Kano

Hukumar lura da shige da fice ta Nijeriya NIS ta bukaci jami’anta da su sake zage dantse gami da inganta ayyukan su.

Shugabar hukumar CSI Kemi Nanna Nandap ce ta bayyana hakan yayin taron bikin daga likkafar jami’an hukumar 450 a shalkwatar hukumar dake jihar Kano.

CSI Nandap wadda ta sami wakilcin shugaban hukumar reshen jihar Kano Ibrahim Muhammad Abubakar lafiya ta bayyana muhimmanci Karin girman gami da sake inganta ayyukan hukumar ga jami’an

Abubakar lafiya ya kara da cewa hukumar ta yi wannan Karin girma ne ga Jami’an saboda hazaka da mayar da hankulansu akan aiki, ba wai dan sun fi kowa bane.

“Wannan Karin girma muka fada musu akan cewa, bawai ko sun fi wasu bane saboda hazakar su ne da kuma kwarewar su a wurin aiki, da kuma suka ci jarrabawa shine Allah ya basu wannan matsayin da yanzu suke kai”

“Muna yi musu murna, muna kuma jan hankalin su da su sake daure damararsu, kasancewar akwai Jan aiki a gabansu a wannan ma’aikata ta shige da fice.

Haka kuma shugaban hukumar ya sake zaburar da jami’an hukumar wajen sanya idanu, don magance harkokin safarar mutane dake addabar nahiyar Afirka da ma kasa baki daya.

Inda ya ce hukumar ta shirya tsaf domin sake fadada ayyukanta a kananan hukumomin jihar Kano 44 don kawo karshen wannan matsala.

“Yanzu haka muna da wani shiri da muke jiran umarni daga sama, domin fara wani aiki kafa shingen bincike a dukkanin mashigar jihar kano da ko wacce kusurwa”

Yace sun dauki wannan mataki domin kada ma wadanda ake safarar a sami damar fita ko shigo da jihar Kano.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp