Home Labarai Ƴan wasan Super Eagles sun sauka a Kano

Ƴan wasan Super Eagles sun sauka a Kano

Ƴan wasan tawagar Super Eagles ta Najeriya sun koma gida Najeriya, inda suka sauka a filin jirgin Malam Aminu Kano da ke jihar Kano.

Wannan ya biyo bayan tirka-tirka da aka samu bayan ƴan wasan sun isa Libya domin fafatawa da abokan karawarsu na ƙasar Libya, duk da cewa hukumar ƙwallon ƙafar ƙasar ta Libya ta ce ba ta da hannu a lamarin.

Najeriya ta je Libya ne domin fafata wasan neman gurbin shiga gasar cin kofin Afirka ta 2025, inda aka samu tsaiko, lamarin da ya haifar da ce-ce-ku-ce musamman a kafofin sadarwa, inda a ƙarshe hukumomi a Najeriya suka buƙaci ƴanwasan su koma gida, sannan ita ma CAF ta ce ta ƙaddamar da bincike a kan lamarin.

Yanzu da ƴan wasan na Najeriya sun sauka a Kano, kamar yadda shafin intanet na tashar talabijin NTA, mallakin gwamnatin Najeriya ya ruwaito.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp