Home Labarai Ƴan wasan Super Eagles sun sauka a Kano

Ƴan wasan Super Eagles sun sauka a Kano

Ƴan wasan tawagar Super Eagles ta Najeriya sun koma gida Najeriya, inda suka sauka a filin jirgin Malam Aminu Kano da ke jihar Kano.

Wannan ya biyo bayan tirka-tirka da aka samu bayan ƴan wasan sun isa Libya domin fafatawa da abokan karawarsu na ƙasar Libya, duk da cewa hukumar ƙwallon ƙafar ƙasar ta Libya ta ce ba ta da hannu a lamarin.

Najeriya ta je Libya ne domin fafata wasan neman gurbin shiga gasar cin kofin Afirka ta 2025, inda aka samu tsaiko, lamarin da ya haifar da ce-ce-ku-ce musamman a kafofin sadarwa, inda a ƙarshe hukumomi a Najeriya suka buƙaci ƴanwasan su koma gida, sannan ita ma CAF ta ce ta ƙaddamar da bincike a kan lamarin.

Yanzu da ƴan wasan na Najeriya sun sauka a Kano, kamar yadda shafin intanet na tashar talabijin NTA, mallakin gwamnatin Najeriya ya ruwaito.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp