Home General Ƴan bindiga sun harbi babban kwamandan dakarun sa kai na jihar Zamfara

Ƴan bindiga sun harbi babban kwamandan dakarun sa kai na jihar Zamfara

'Yan Ta'adda

A Wata musayar wuta da aka yi a tsakanin ƴan bindiga da dakarun tsaro na sakai CPG a jihar Zamfara dake Arewacin Najeriya, ƴan ta’addar sun kashe mutane dama inda suka raunata wasu cki har da babban kwamandan rundunar ƴan sa kan Janar Lawal B. Muhammad mai ritaya.

Rahotanni dai sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun tare hanyar Funtua zuwa Tsafe ne mai cike da cunkoson jama’a da yammacin ranar lahadi, inda suka far wa masu ababen hawa ciki har da Darakta janar na hukumar ta CPG.

Sannan a yayin wannan samamen ƴan bindigar sun yi  awun gaba da wasu fasinjoji da dama dake kan hanyarsu ta zuwa wurare daban-daban.

Wata majiya daga ma’aikatar tsaron cikin gida ta jihar Zamfara, wadda ta bukaci a sakaya sunanta, ta tabbatar da faruwar lamarin, ta kuma ce shugaban na samun kulawa a wani asibiti da ke Gusau, babban birnin jihar.

Wannan arin na zuwa ne kwanaki kadan bayan da ‘yan bindiga suka kashe jami’an na CPG akalla takwas da wani direban motar  sufuri a karamar hukumar Tsafe da ke jihar ta Zamfara.

Shaidun gani da ido sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun yi wa jami’an na CPG kwanton bauna ne kafin su an kara suka bude musu wuta.

Da yake bayani game da harin, babban kwamandan da aka harba ya bayyana cewa, bayan da ya fahimci cewa ‘yan bindigar na shirin kai hari a tsafe, sai ya tura jami’an CPG 105 zuwa karamar hukumar tare da ajiye su a wannan wuri domin baiwa matafiya kariya ba tare da sanin sun musu riga Malam masallaci ba.

Sai gashi abin bakin ciki ƴan bindigar sukai musu kwanton bauna saboda sun kwana a wurin, a yayin da dakarun sa kan suke sauka sai suka bude musu wuta kuma suka kashe wasu daga cikinsu tare da jikkata wasu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
An Zargi Kwankwaso da Sayen Fom ɗin Takara na Kujeru 69 a Jam'iyyar PRPƘasurgumin ɗan bindiga, Turji ya ɗauki Alhakin Kashe Sojoji a Jihar SokotoMasu Iƙirarin Jihadi Sun Hallaka Manoma 11 a Jihar Borno 'Yan Bindiga sun ƙone shingen Jami'an NSCDC Tare da Garkuwa da Mutum 1 a Jihar KebbiTaron NUJ: Lokacin Da Manyan Jami’an Tsaro Suka Guji Yan Jarida Daga Yushau A. ShuaibSamar da Tsaro: Sojojin Najeriya sun Kama ƴan ƙasashen Wajen 46Ta'addanci: Za a Gurfanar da Mutane 400 a Gaban Kotun Tarayya da ke AbujaAn Ceto Matar Janar Rabe da ya Rasu a Hannun ƴan BindigaHauhawar Farashin Kayan Masarufi a Najeriya ya ƙaru Zuwa Kashi 15.93Rundunar Sojin Najeriya ta Gudanar da Hare-Hare Kan Maɓoyar ƴan Bindiga a Jihar KatsinaZaben 2027: NDC ta Tsayar da Ɗan Kwankwaso Mataimakin ɗan Takarar Gwamnan KanoKotu ta Umarci INEC da ta Soke Rajistar ADC Tare da Jam’iyyu 4Manyan Tsofaffin Jami'an Soji 10 da Suka Rasa Rayukansu a Hannun ƴan Ta'addaTarihin Rayuwar Janar Rabe da ya Rasu a Hannun ƴan BindigaMatsalar Tsaro: Masu Zanga-Zanga Sun Tare Babbar Hanyar Abuja
X whatsapp