Home Labarai ko mene yasa aka kwana ba wutar lantarki ranar litinin a Nijeriya

ko mene yasa aka kwana ba wutar lantarki ranar litinin a Nijeriya

Najeriya ta sake fuskantar katsewar wutar lantarki sakamakon lalacewar babban layin lantarki na ƙasar a ranar Litinin.

Layin ya lalace ne da misalin ƙarfe 7 na yamma, kamar yadda sanarwa daga kamfanin rarraba lantarki ta ƙasa (TCN) ya bayyana.

Lamarin ya jefa miliyoyin ‘yan ƙasar da kuma sana’o’insu cikin duhu.

Wannan dai shi ne karo na biyar da layin ke lalacewa a shekarar 2024.

Shi ma kamfanin rarraba hasken wutar lantarki reshen jihar Kano (KEDCO) ya nemi afuwar kwastomominsa kan abin da ya faru a wani sako da ya wallafa a shafinsa na X.

“Muna bakin cikin sanar da ku cewa an samu ɗaukewar wuta ne sakamakon matsalar da aka samu a layin wuta na ƙasa,” kamar yadda shugaban sashen sadarwa na kamfanin Sani Bala ya bayyana.

Ya ce hakan ne ya janyo rashin rarraba wutar zuwa ga kwastomomi.

“Muna rokon al’umma da su yi hakuri yayin da muke ci gaba da aiki tukuru don shawo kan matsalar ta faru da kuma mayar da wutar lantarki yadda muka saba,” in ji shi.

Ya buƙaci mutane da su kula sosai wajen kare kai daga masu sata ko lalata wayoyin wutar lantarki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp