Home General Fashewar tankar mai ta kashe sama da mutum 100 a jihar Jigawa

Fashewar tankar mai ta kashe sama da mutum 100 a jihar Jigawa

Wata tanka ɗauke da man fetur ta yi sanadiyyar kashe sama da mutum 100 a jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya bayan ta faɗi tare da kamawa da wuta.

Babbar jami’ar hukumar kiyaye haɗurra a Jigawa, Aishatu Sa’adu, ta ce zuwa yanzu mutum 104 ne suka mutu sakamakon hatsarin da ya faru ranar Talata da dare.

Da take magana yayin da ta isa wurin da lamarin ya faru a garin Majiya na ƙaramar hukumar Taura, Aisha ta ce wasu mutum 100 sun jikkata.

Tun da farko ta ce ibtila’in ya faru ne bayan da direban tankar ya kauce wa wata babbar mota ɗauke da tumatur.

Hakan ya sa direban tankar ya faɗa gefen titin har kan motar ya rabu da gangar jikinta, lamarin da ya sa fetur ɗin da yake dako ya malale titi da kwatoci a gefen hanyar.

Kakakin rundunar ‘yansanda a Jigawa, DSP Lawan Adam, ya ce ganin haka ne ya sa mutane suka yi dafifi a wurin da lamarin ya faru domin kwasar man da ya zuba a ƙasa bayan sun ci ƙarfin jami’an tsaron da ke korarsu a ƙokarin kauce wa tashin gobara.

Shaidu sun shaida wa BBC cewa tankar ta yi kusan awa biyu tana ci da wuta kafin jami’an kashe gobara su yi nasarar kashe ta.

Zuwa yanzu ana shirin yin jana’izar mutanen da suka mutu sakamakon fashewar tankar.

Hotunan da aka turo wa BBC sun nuna yadda aka lulluɓe gawarwakin mutanen da ganyayyaki, yayin da wasu hotunan suke ɗauke da gawarwakin da suka rasa wasu sassa na jikinsu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp