Home Labarai Gwamnatin Najeriya da ƴan ƙwadago sun tashi taro babu matsaya kan tsadar...

Gwamnatin Najeriya da ƴan ƙwadago sun tashi taro babu matsaya kan tsadar rayuwa

Ba a cim ma matsaya ba a taron tattaunawa tsakanin haɗaɗɗiyar ƙungiyar ƙwadago da gwamnatin Najeriya game da tsadar rayuwa a ƙasar da ƙarin farashin mai ya haifar.

Kafofin yaɗa labarai sun ruwaito shugabannin ƙungiyar ma’aikata ta NLC da ta ‘yankasuwa TUC sun gana da wakilan gwamnatin tarayya a ofishin sakataren gwamnati da ke Abuja ranar Alhamis.

Ministan yaɗa labaran Najeriya, Mohammed Idris, ya shaida wa manema labarai a ƙarshen taron cewa taron alama ce da ke nuna yadda gwamnati ta mayar da hankali wajen tattaunawa da ƴan ƙwadago a kan batun.

Sai dai kuma ministan ya ƙi faɗar abubuwan da aka tattauna a wajen taron, yana mai cewa gwamnati ba za ta zura ido har sai abubuwa sun lalace ba sannan ta gana da ƙungiyoyin ƙwadagon.

“An tattauna abubuwa da dama amma kamar yadda na faɗa tun farko, har yanzu ana cikin sasanci ne, kuma wannan harka ce da ba za a iya gamawa a zama ɗaya ba, kuma kawo yanzu ba mu cim ma wani abu da za a iya faɗa wa ƴan Najeriya ba,” in ji shi.

Ƴan Najeriya da dama sun bayyana rashin jin daɗinsu kan ƙarin farashin man fetur da aka yi kwanan nan a ƙasar, da kuma tsadar rayuwa da ake fama da ita.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp