Home Labarai Rundunar ‘Yan sandan Jihar Kano ta Kama Dan Sandan Bogi a jihar

Rundunar ‘Yan sandan Jihar Kano ta Kama Dan Sandan Bogi a jihar

Rundunar  ‘yan sandna jihar kano ta sami nasarar kama wani matashi da take zargin da yin sojan gona, matsayin dan sandan bodi a jihar dake arewa maso yammacin Nijeriya.

Wannan na cikin wata sanarwa da Kakakin rundunar na kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar aka rabawa manema labarai a jihar a daren Alhamis, inda ya ce sun kama shi ne biyo bayan koken da al’umma suke yi a Kansa.

A cewar Kiyawa, “Mun kama wani matashin Salisu Bala mazaunin unguwar Kurna, a sakamakon yadda yake sojan gona da kakin ‘Yan Sanda yana karbar kudi a hannun al’umma da sunan shi Dan Sandan Sarauniya ne”.

Kuma dai yana gudanar da wannan aika-aikar tasa ne a unguwannin Sabon Gari, Fagge, Koki dake kwaryar birnin Kano.

To sai dai bayan kamo shi da aka yi bisa umarnin Kwamishinan ‘Yan Sandan Kano, CP Salman Dogo Garba, an gano kayan ‘Yan Sanda hudu a gidansa, a inda daga bisani ya tabbatar da cewa yana ta’ammali da kayan maye.

domin haka ne CP Dogo Garba ya ce ba zasu dagawa masu aikata sojan gona da sunan rundunar ko kuma ‘Yan Sandan Sarauniya ba domin haka rundunar ta bayar da wannan lambar waya (07038188127), domin al’umma su shigar da korafi akan ‘Yan Sandan dake musguna musu.

A karshe rundunar ta kuma bada lambobin wayar da za’a bada rahoton dukkan wani abu da ba’a gamsu da shi ba, 08032419754, 08123821575.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp