Home General Janye tsare-tsaren Tinubu zai kawo cikas ga Najeriya – Bankin Duniya

Janye tsare-tsaren Tinubu zai kawo cikas ga Najeriya – Bankin Duniya

Bola Ahned Tinubu

Bankin Duniya ya yi gargaɗin cewa muddin gwamnatin tarayya ta janye tsare-tsaren tattalin arziki da ta fara, to hakan zai iya janyo babbar cikas ga Najeriya.

Babban wakilin bankin a Najeriya, Dr Ndiame Diop, shi ya yi wannan gargaɗi ranar Alhamis a Abuja yayin kaddamar da wani rahoto kan ‘Cigaban Najeriya da kuma ɗorewarta’ a daidai lokacin da ƙasar ke fuskantar matsaloli.

Diop ya ce dole ne a ɓullo da tsare-tsaren domin ɗorewar Najeriya, duk da cewa za su janyo tsadar rayuwa da kuma wahalhalu ga ƴan ƙasar.

“Janye waɗannan tsare-tsare zai jefa Najeriya cikin barazana da kuma tawayar tattalin arziki,” in ji Diop.

Ya ce ƙarin kuɗaɗen shiga da gwamnatin tarayya ta samu a watannin farko na wannan shekara ya faru ne sakamakon cire tallafin man fetur da na kuma na canjin kuɗin waje, inda ya ce hakan ya nuna dole ne a ci gaba da tsare-tsaren.

Tun a lokacin rantsuwar kama aiki ne, shugaba Bola Tinubu ya sanar da janye tallafin man fetur, abin da ya jefa ƴan Najeriya da dama cikin kunci da wahalhalu musamman ma masu karamin karfi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp