Home Labarai Rushe shugabancin KANSIEC ya haifar da cece-kuce a jihar Kano

Rushe shugabancin KANSIEC ya haifar da cece-kuce a jihar Kano

Majalisar jihar Kano
Majalisar jihar Kano

Majalisar dokokin jihar Kano ta tabbatar da cewa za a gudanar da zaben kananan hukumomi kamar yadda aka tsara a ranar Asabar 26 ga watan Oktoba, 2024, duk da hukuncin da babbar kotun tarayya ta yanke na hana hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar Kano KANSIEC gudanar da zaben.

Wannan matsaya ta biyo bayan hukuncin da mai shari’a Simon Amobeda na babbar kotun tarayya da ke Kano ya yanke a ranar Talata,

Kotu tace wadanda aka bawa mukamin shugabannin hukumar basu cancanta saboda sun kasance magoya bayan jamiyyar NNPP mai mulkin Kano, dan haka kotun tace wadannan mutane basu da damar gudanar da zaben Ƙananan.
Sai dai gwamnatin jihar Kano ta bayyana kudirinta na ci gaba da gudanar da zaben, ko da kuwa hukumomin tsaro irin na ‘yan sanda ba sa iya ba da kariya.

Shugaban masu rinjaye na majalisar, Lawan Hussaini Dala, ya soki hukuncin kotun, yana mai cewa ya sabawa umarnin da mai shari’a Nura Ma’aji ya bayar a baya, wanda ya haramtawa jam’iyyun siyasa 19 ciki har da jam’iyyar All Progressives Congress (APC) kalubalantar zabe.

“Hukuncin da kotun tarayya ta yanke na tsige shugaban KANSIEC ya ci karo da hukuncin da Mai shari’a Ma’aji ya yanke na hana jam’iyyun siyasa kutsawa cikin harkokin zabe,” in ji Dala.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp