Home Labarai Sojojin Najeriya biyar sun mutu a haɗarin mota a jihar Filato

Sojojin Najeriya biyar sun mutu a haɗarin mota a jihar Filato

Wasu sojojin sama na Najeriya biyar na daga cikin matafiya 19 da suka rasu a wani mummunan haɗarin mota da ya auku a Hawan Kibo da ke ƙaramar hukumar Riyom ta jihar Filato a jiya Talata.

A wata sanarwa da kakakin rundunar sojin sama ta Najeriya, Olusola Akinboyewa ya fitar, ya ce, sojojin na kan hanyarsu ne ta zuwa wani wasa a Abuja, lokacin da motarsu ta yi taho-mu-gama da wata babbar mota.

Sai dai kuma wani bayani da hukumar kiyaye haɗura ta Najeriya ta fitar ya saɓa da wanda kakakin sojin ya fitar, inda hukumar ta ce motar bas ta sojojin ƙirar Hiace, mai ɗaukar mutum 18 da ta taso daga Yola ta bi yo ta Jos a kan hanyarta ta zuwa Abuja ta ci karo ne da tirela wadda ke tsaye a kan hanya, lamarin da ya janyo mutuwar direban da dukkanin sauran mutanen da ke cikin motar su 18.

A wata hira da tasahar talabijin ta Channels, kakakin hukumar ta kiyaye haɗura (FRSC) a jihar ta Filato, Peter Longsan, ya ce dukkanin mutanen da ke cikin wannan mota bas da sojojin suke sun mutu.

Longsan ya danganta munin haɗarin da ya kai ga mutuwar mutanen gaba ɗaya, da gudun da direab bas ke yi inda ya ce a dalilin hakan ne da ta yi karo da tirelar ba wanda ya tsira.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp