Home Labarai Kwastam ta kama fatar jaki 180 a jihar Kebbi

Kwastam ta kama fatar jaki 180 a jihar Kebbi

Jami’an hukumar hana fasa kwauri a jihar Kebbi sun sami nasarar kama fatar jaki 180 da ake yunƙurin yin fasa-ƙwaurinta.

Kwamandan rundunar a jihar Kebbi, Iheanacho Ojike, shi ya bayyana haka yayin zantawa da manema labarai.

Ya ce sauran kayaki da suka kwace sun haɗa da litar man fetur har guda 16,300 da tufafi da kuma katan-katan guda 74 na wasu magunduna daban-daban wanda kuɗin fitonsu ya kai sama da naira miliyan 300.

Iheanacho ya ce an yi samu nasarar kama kayan ne bisa irin ƙoƙari da jami’an hukumar suke yi wajen kakkaɓe masu aikata ɓarna.

Kwamandan hukumar ya ce wasu mutane na amfani da lokacin tsadar man fetur wajen safararsa zuwa waje.

Ya ƙara da cewa an kama wasu mutane biyar da ake zargi da hannu a fasa kwaurin kayakin.

Ya kuma gargaɗi masu fasa kwauri da su daina domin jami’ansu a shirye suke wajen cafke su.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp