Home General Kwankwaso ya magantu kan matsalar wutar lantarki a Arewacin Nijeriya

Kwankwaso ya magantu kan matsalar wutar lantarki a Arewacin Nijeriya

Tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya bayyana rashin jin daɗinsa kan rashin wutar lantar a mafi yawan jihohin Arewa.

Kamar yadda ya rubuta a shafinsa na X, Kwankwaso ya ce, “Abin takaici ne a ce mafi yawan yankunan Arewa suna zaune cikin duhun rashin wutar lantarki saboda tangarɗa a layin lantarkin 330kV wanda ya ɗauko wuta daga Shiroro zuwa Kaduna, wanda shi ne yake ba jihohin Kano da Kaduna, da layin da yake ba Bauchi da Gombe da wasu jihohin arewa maso gabas wuta.

“Matsalar ta ƙara ta’azzara ne saboda yanayin tsadar man fetur da ake ciki a Najeriya, wanda ya tilasta wa kamfanoni da kasuwanci da dama suka durƙushe.

Sannan lokacin da aka ɗauka ba a magance matsalar ba, ya nuna cewa akwai matsala a ɓangaren makamashin Najeriya,” in ji shi, inda ya ƙara da cewa akwai buƙatar a ɗauki mataki domin guje wa sake aukuwar lamarin, ta hanyar nemo wasu hanyoyin makamashin.

“Ina ba jihohin da ƴan kasuwa shawarar su zuba kuɗi a wasu hanyoyin samar da makamashin domin rage ta’allaƙa da hanyar makamashi guda ɗaya,” in ji Kwankwaso.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp