Home AFIRKA An rantsar da Kithure a matsayin sabon mataimakin shugaban ƙasar Kenya

An rantsar da Kithure a matsayin sabon mataimakin shugaban ƙasar Kenya

Wannan ya biyo bayan hukuncin kotu da ya bada damar rantsar da sabon mataimakin biyo bayan tsige tsohon mataimakin shugaban ƙasar Rigathi Gachagua a watan da ya gabata.

Babbar kotu a Kenya ce ta dakatar da rantsar da Kindiki bayan Gachagua da magoya bayansa sun shigar da ƙarar ƙalubalantar tsigeshi da majalisun dokokin ƙasar biyu suka yi.

To sai dai  a ranar Alhamis kotu ta janye dakatarwar da aka yi na rantsar da Rigathi Gachagua a matsayin sabon mataimakin shugaban ƙasar Kenya.

Kotun ƙoli a Kenya ce ta bayar da umarnin rantsar da sabon mataimakin shugaban ƙasa, bayan majalisun dokokin ƙasar biyu suka tsige Rigathi Gachagua daga muƙaminsa.

An dai share tsawon watanni ana fama da rikici tsakanin Shugaba William Ruto da mataimakinsa Rigathi Gachagua, to sai dai a ranar 17 ga watan oktoban da ya gabata rikicin ya ɗauki sabon salo inda har ta kai ƙarama da kuma babbar majalisar dokokin dokokin ƙasar suka kaɗa ƙuri’ar kawo ƙarshen mulkinsa.

Wanda ake shirin rantsarwa a wannan juma’a wato ministan cikin gida Kithure Kindiki, mutum ne mai shekaru 52 a duniya, kuma ya yi fice saboda kasancewarsa kasaitaccen malamin jami’a, kafin daga bisani ya tsunduma siyasa daga-gadan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp