Home General Zanga – Zanga -Atiku ya magantu kan gurfanar da yara a gaban...

Zanga – Zanga -Atiku ya magantu kan gurfanar da yara a gaban Kotu

Jogaran adawar Najeriya, Atiku Abubakar ya soki gwamnatin ƙasar, kan abin da ya kira gurfanar da ƙananna yara a gaban kotu domin yi musu shari’a.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa X, tsohon mataimakin shugaban ƙasar, ya ce ya damu da bidiyon yaran da aka nuna ”bayan yunwa ta yi musu illa, a inda aka tsare su”.

”Wannan abu na tayar da hankali ya tunamin da zaluncin ‘yan aƙidar Nazi, tare da ƙara fito da yadda gwamnati ke wasarere da rayukan mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba, musamman ƙananan yara”, in ji Atiku Abubakar.

Ya ce kundin tsarin mulkin Najeriya ya bai wa ƙananan yara cikakken ‘yancin mutuntawa, amma abin mamakin sai suka rasa hakan a Najeriya, a cewar Atikun.

”Ina mamakin mutumin da ke iƙirarin kare dimokraɗiyya, har ya jagoranci zanga-zanga a baya, amma a yanzu yake barazana ga waɗanda ke yunƙurin nuna damuwarsu kan halin da suka shiga sakamakon manufofinsa masu tsauri”, in tsohon ɗan takarar shugabancin ƙasar.

Ya ƙara da cewa ƙananan yaran -waɗanda su ne suka fi cutuwa kan manufofin gwamnatin Tinubun na da damar gudanar da zanga-zangar lumana kamar yadda kundin tsarin mulkin ƙasar ya ba su dama.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp