Home General Zanga – Zanga -Atiku ya magantu kan gurfanar da yara a gaban...

Zanga – Zanga -Atiku ya magantu kan gurfanar da yara a gaban Kotu

Atiku

Jogaran adawar Najeriya, Atiku Abubakar ya soki gwamnatin ƙasar, kan abin da ya kira gurfanar da ƙananna yara a gaban kotu domin yi musu shari’a.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa X, tsohon mataimakin shugaban ƙasar, ya ce ya damu da bidiyon yaran da aka nuna ”bayan yunwa ta yi musu illa, a inda aka tsare su”.

”Wannan abu na tayar da hankali ya tunamin da zaluncin ‘yan aƙidar Nazi, tare da ƙara fito da yadda gwamnati ke wasarere da rayukan mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba, musamman ƙananan yara”, in ji Atiku Abubakar.

Ya ce kundin tsarin mulkin Najeriya ya bai wa ƙananan yara cikakken ‘yancin mutuntawa, amma abin mamakin sai suka rasa hakan a Najeriya, a cewar Atikun.

”Ina mamakin mutumin da ke iƙirarin kare dimokraɗiyya, har ya jagoranci zanga-zanga a baya, amma a yanzu yake barazana ga waɗanda ke yunƙurin nuna damuwarsu kan halin da suka shiga sakamakon manufofinsa masu tsauri”, in tsohon ɗan takarar shugabancin ƙasar.

Ya ƙara da cewa ƙananan yaran -waɗanda su ne suka fi cutuwa kan manufofin gwamnatin Tinubun na da damar gudanar da zanga-zangar lumana kamar yadda kundin tsarin mulkin ƙasar ya ba su dama.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp