Home General MDD ta yi gargaɗin samun matsananciyar yunwa a Najeriya a 2025

MDD ta yi gargaɗin samun matsananciyar yunwa a Najeriya a 2025

Ofishin Majalisar Dinkin Duniya, mai lura da al’amuran jin ƙai ya yi hasashen samun matsananciyar yunwa a Najeriya da wasu ƙasashen Afirka.

Cikin wani saƙo da ofishin ya wallafa a shafinsa na X, ya yi gargaɗin samun tsanantar matsalar a Najeriya tsakanin watan Nuwamban 2024 zuwa watan Mayun 2025.

”Ya kamata a ɗauki matakai domin yaƙi da yunwa da ceto rayukan mutane a yanzu da kuma tsawon lokaci a nan gaba”, kamar yadda ofishin ya wallafa.

Bayanan da ofishin ya fitar sun nuna cewa a NAjeriya, mutum miliyan 38 ne za su fuskanci matsalar, yayin da ƙasar Sudan ta Kudu ke biye mata da mutum miliyan 21, sai ƙasar Ethiopia mai mutum miliyan 15.

A farkon wannan shekarar ne dai gwamnatin Najeriya ta sanar da wasu matakai uku na kawo sauƙi ga matsalar ƙarancin abinci a ƙasar.

Ɗaya daga cikin matakan shi ne, gwamnatin ta fito da tan 42,000 na abinci daga rumbunan ma’aikatar harkokin noma da nufin kawo sauƙi ga al’ummar ƙasar.

Haka kuma gwamnatin ta ce idan har matsalar ta faskara za ta iya ɗaukar matakin shigar da abinci daga ƙasashen waje domin magance tsadar abinci a faɗin ƙasar.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Samar da Tsaro: Sojojin Najeriya sun Kama ƴan ƙasashen Wajen 46Ta'addanci: Za a Gurfanar da Mutane 400 a Gaban Kotun Tarayya da ke AbujaAn Ceto Matar Janar Rabe da ya Rasu a Hannun ƴan BindigaHauhawar Farashin Kayan Masarufi a Najeriya ya ƙaru Zuwa Kashi 15.93Rundunar Sojin Najeriya ta Gudanar da Hare-Hare Kan Maɓoyar ƴan Bindiga a Jihar KatsinaZaben 2027: NDC ta Tsayar da Ɗan Kwankwaso Mataimakin ɗan Takarar Gwamnan KanoKotu ta Umarci INEC da ta Soke Rajistar ADC Tare da Jam’iyyu 4Manyan Tsofaffin Jami'an Soji 10 da Suka Rasa Rayukansu a Hannun ƴan Ta'addaTarihin Rayuwar Janar Rabe da ya Rasu a Hannun ƴan BindigaMatsalar Tsaro: Masu Zanga-Zanga Sun Tare Babbar Hanyar AbujaDuk Wanda aka Kama Yana Kasuwanci da 'Yan Ta'adda, za a ɗauke shi a Matsayin ɗan ta’adda - Christopher MusaFarashin ɗanyen Mai ya Faɗi Bayan Amurka ta Soke Sabbin Hare-Haren kaiwa IranAmurka ta yi sulhu kan yaƙin da ta ke yi da Iran - TrumpMajalisar Wakilan Najeriya ta Amince da ƙudirin Dokar Kafa ’Yan sandan JihaHukuncin da aka Yanke wa Masu Alaƙa da Sace ɗaliban Jihar Neja
X whatsapp