Home General COAS Lagbaja ya mutu yana da shekaru 56

COAS Lagbaja ya mutu yana da shekaru 56

Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya bayyana mutuwar shugaban rundunar sojin Nijeriya Laftanar Janar Taoreed Abiodun Lagbaja, wanda ya mutu yana da shekaru 56 a duniya.

Wannan na cikin wata sanarwa da masawarci na musamman ga shugaban kasar kan harkokin yada labarai Bayo Onanuga ya fita, aka raba manema labarai a birnin tarayya Abuja.

Jaridar PRNigeria ta ruwaito cewa Taoreed Abiodun Lagbaja ya mutu a daren talata bayan fama da rashin lafiya.

An haifi Taoreed Lagbaja a 28 ga watan Fabrerun 1968, sannan shugaban kasa Asiwajo Bola Ahmad ya nadashi matsayin Hafsan sojojin Najeriya a ranar 19 ga watan Yunin 2023.

ya fara aiki da rundunar sojin kasar ne bayan daukar horo a kwalejin sojojin kasar ta Nigerian Defence Academy a 1987, in da a ranar 19 ga watan satumba 1992, ya fito a matsayin Second Lieutenant rukuni na 39 (39th Regular Course).

a yayin aikinsa Lt. General Lagbaja ya nuna gogewa da shugabanci na gari gami da sadaukar a matsayin kwamandan bataliya ta 72 rukunin sojoji na musamman.

ya kuma taimaka matuka wajen gudanar da ayyukan tsaron cikin gida, wanda ya hadar da jagarantar dakarun OPERATION ZAKI a jihar Benue, Lafiya Dole a jihar Borno, Udoka a kudancin Nijeriya, da Operation Forest Sanity a yankin Jihohin Kaduna da Niger.

haka kuma ya halarci kwalejin sojoji ta Amurka in da ya yi sami digiri na II a dabaru wato “Strategic Studies” wanda hakan ya bashi damar nuna sadaukarwa da kwarewa gami na son cigaban harkokin shugabancia a ayyukan soji.

Lt. General Lagbaja yana da Mata daya Mai suna Mariya da ‘ya’ya guda biyu.

daga bisani shugaba Tinubu ya mika ta’aziyyarsa ga iyalai da rundunar sojin Nijeriya bisa wannan rashi ya kuma yi masa addu’a da kasa baki daya.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp