Home General Atiku yayi martani ga fadar shugaban kasa kan batun hassada

Atiku yayi martani ga fadar shugaban kasa kan batun hassada

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar ya ce ba ya yi wa Tinubu hassada, inda ya ce ya jefa ƴan Najeriya cikin kunci.

Ɗan takarar shugaban ƙasar karkashin jam’iyyar PDP a zaɓen 2023, na mayar da martani kan kalamai da fadar shugaban Najeriyar ta yi cewa yana ƙyashi tare da baƙin ciki da matsayin Shugaba Bola Tinubu na shugaban ƙasa.

Wata sanarwa da mai bai wa shugaban ƙasar shawara kan harkokin yaɗa labarai, Bayo Onanuga ya fitar ranar Lahadi, ya soki Atiku kan ci gaba da sukar tsare-tsaren tattalin arzikin da shugaban, maimakon mayar da hankali kan matsalolin jam’iyyarsa.

Tsohon mataimakin shugaban ƙasar dai ya sha sukar tsare-tsare da gwamnatin Tinubu ta ɓullo da su, musamman na tattalin arziki, inda ya ce babu abin da za su haifar illa jefa ƴan Najeriya cikin kunci da wahala.

Wata sanarwa da mai taimakawa Atiku na musamman kan yaɗa labarai Phrank Shaibu ya fitar ranar Litinin, Atiku ya ce sai Tinubu ya aiwatar da tsare-tsare kafin yake duba illolin da za su haifar.

“Tinubu bai shiryawa mulki ba. Sai ya aiwatar da abu kafin yake duba illarsa daga baya. Wannan shi ya sa ya sanar da janye tallafin man fetur ba tare da kawo abin da zai rage wa ƴan ƙasar raɗaɗi ba.

“Abin mamaki ne a yi iƙirarin cewa Atiku na kyashin Tinubu. Ba zai yi hassada da Tinubu ba saboda irin kunci da ya jefa ƴan Najeriya,” in ji sanarwar.

Atiku ya ce babu wani adalin shugaba wanda yake da zimmar ganin ƴan Najeriya cikin walwala da zai yi hassada da irin gallazawa da ake yi musu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp