Home General IPMAN ta cimma matsaya da Dangote kan sayen fetur

IPMAN ta cimma matsaya da Dangote kan sayen fetur

Ƙungiyar dillalan man fetur mai zaman kanta ta Najeriya IPMAN ta ce mambobinta sun cimma matsaya domin fara sayen man fetur daga matatar man Dangote kai-tsaye.

Shugaban ƙungiyar ta IPMAN na ƙasa, Abubakar Garima, shi ya bayyana haka a Abuja ranar Litinin bayan uwar ƙungiyar ta gudanar da taro da mambobinta.

Ya ce haɗin gwiwa da Dangote zai saka a samu wadataccen man fetur cikin sauki a faɗin ƙasar.

“Ina farin cikin sanar da cewa matatar Dangote ta amince ta fara sayar mana da man fetur da kuma dizel kai-tsaye domin rarrabawa a defo-defo ɗin mu da kuma sauran gidajen mai,” in ji Girima.

Ya buƙaci mambobin IPMAN ɗin da su mara wa matatar Dangote baya, inda ya ce hakan zai kuma farfaɗo da yanayin hada-hadar man fetur da kuma rage ƙarancinsa da ake samu a ƙasar.

Abubakar ya ce matakin zai kuma janyo bunƙasar ɓangaren man fetur ɗin Najeriya.

Matatar ta Dangote ta yi alkawarin fara sayar da man fetur ɗin ga mambobin IPMAN sama da 30,000 da kuma gidajen mai 150,000 a faɗin ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp