Home General Gwamnatin Najeriya ta amince da kasafin kuɗin 2025

Gwamnatin Najeriya ta amince da kasafin kuɗin 2025

Majalisar zartaswar Najeriya ta amince da kasafin kuɗin ƙasar na 2025 da ya kai naira tiriliyan 47.9.

Ministan kasafin kuɗi da tsare-tsare, Atiku Bagudu ne ya bayyana haka ranar Alhamis bayan kammala taron majalisar da shugaba Bola Tinubu ya jagoranta.

Kasafin kuɗin ya ƙunshi manyan ayyuka da kuma na musamman da za a gudanar a faɗin ƙasar.

“Mun amince da kasafin kuɗin, kuma za a miƙa shi gaban majalisar dokoki ta ƙasa domin yin nazari da kuma amincewa da shi,” in ji Bagudu.

Ya kuma ce za a ciyo sabon rancen da ya kai naira tiriliyan 9.2 don cike giɓin kasafin kuɗin na shekarar 2025.

Ya ce an yi hasashen samun bunƙasar yawan kayayyakin da ake samarwa a cikin gida da kashi 4.6 cikin 100.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp