Home General Tinubu ya bai wa firaministan Indiya lambar yabo ta GCON

Tinubu ya bai wa firaministan Indiya lambar yabo ta GCON

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karrama firaministan Indiya, Narendra Modi da lambar yabo ta biyu mafi daraja a ƙasar wato GCON.

Tinubu ya bayyana hakan ne a lokacin ganawa da Mista Modi a fadar gwamnatinsa da ke Villa a Abuja.

A ranar Asabar da daddare ne firaministan na Indiya ya isa Najeriya a wata ziyara ta kwana guda da zai yi a ƙasar

Shugaban na Najeriya ya ce ya bai wa Modi lambar girmamawar ce domin ”nuna godiyarmu ga Indiya a matsayin ƙawar Najeriya”.

Ziyarar Modin ita ce ta farko da wani firaministan Indiya ya kai wa Najeriya tun 2007, lokacin da Firaminitan na wancan lokaci Dakta Dr Manmohan Singh ya kai ƙasar.

Shugabannin biyu za su mayar da hankali a tattaunawarsu wajen ƙarfafa dangantaka tsakanin ƙasashen biyu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp