Home General Gwamnatin Kano ta zargi alkali Amobeda

Gwamnatin Kano ta zargi alkali Amobeda

Gwamnatin Jihar Kano ta zargi Mai shari’a Simon Amobeda na Babbar Kotun Tarayya da nuna son zuciya a shari’ar zaben kananan hukumomi da aka gabatar gabansa.

Jam’iyyar APC ce dai tare da wasu masu ruwa da tsaki su ka shigar da kara su na neman kotu ta bayyana cewa ba a samu zababbun shugabannin kananan hukumomi ba a jihar Kano.

Jaridar GUARDIAN ta rawaito cewa a zaman fara sauraren korafe-korafen da aka shigar a jiya Juma’a, Antoni Janar na Jihar Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Isa Haruna Dederi, ya nemi Mai Shari’a Amobeda ya janye kansa daga shari’ar saboda zargin nuna son zuciya da ya ce alkalin ya yi a lokuta da dama a kan gwamnatin Kano.

A cikin takardar da ya gabatar, Dederi ya yi zargin cewa mai shari’ar yana da wata kiyaiya a zuciyar shi da ya nuna ga gwamnatin jihar da hukumominta tun bayan da aka shigar da wani korafi ga Hukumar Kula da Alkalai ta Kasa (NJC) da ke zarginsa da cin gajiyar iko da kuma bayar da umarni ba bisa ka’ida ba.

Gwamnatin jihar ta bayyana cewa ta lura da “wadansu abubuwan da ba su dace ba” musamman game da shari’o’in da suka shafi mutanen da ke da alaka da siyasa, musamman wadanda ke cikin jam’iyyun adawa, da aka gabatar gabansa. Wannan, a cewar gwamnatin, yana nuna wata alaka tsakanin mai shari’ar da wata jam’iyyar adawa.

Gwamnati ta kuma ce “Mai shari’ar ya sha fitowa a jaridu yana barazanar fallasa wani jami’in gwamnatin Jihar Kano da ya rubuta karar a kansa, yana nuna fushinsa tare da kokarin tabbatar da cewa karar ba ta dace ba.”

Duk da haka, Mai shari’a Amobeda, yayin nuna rashin amincewa da bukatar da gwamnatin ta gabatar na ya janye kansa daga shari’ar, ya ce ba ya goyon bayan wani bangare kamar yadda ake zarginsa, sai dai yana goyon bayan adalci ne kawai.

Mai shari’ar, yana martani, ya ce, “Lauyoyi marasa kwazo ne kawai ke gabatar da bukatar alkali ya janye kansa daga shari’a,” sannan ya zargi lauyoyin Jihar Kano da yin “abubuwa marasa kyau” a kansa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp