Home General Gwamnatin Kano ta mayarwa da Jami’ar Northwest sunanta

Gwamnatin Kano ta mayarwa da Jami’ar Northwest sunanta

Gwamnatin jihar Kano Ta Dawowa Da Jami’ar Yusuf Maitama University sunanta na Asali wato Northwest University.

Cikin wata sanarwa da kwamishinan ma’aikatar ilimi mai zurfi ta jihar Kano Dr. Yusuf Kofar mata ya wallafa a shafinsa na facebook.

Ya ce, a zaman majalisar zartarwar jihar kano na 21 da ya gudana karkashin jagorancin gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf, majalisar ta amince da maidawa da jami’ar sunanta na asalai wato NORHTWEST UNIVERSITY, KANO

Kazalika majasar zartarwar ta amince a sanya sunan na Yusuf Maitama Sule a abuwar kolejin ilimi ta ƙaramar hukumar Ghari domin girmamawa ga mai sunan.

Kofarmata ya kuma bayyana cewa tuni aka bayar da umarnin tura waɗannan kuduri zuwa majalisar dokoki ta jihar Kano domin zamar da su doka, ciki harda gyaran dokar shekarun aiki na manyan makarantu daga shekaru 65 zuwa 70 ga farfesoshi na jami’a, da kuma 60 zuwa 65 na sauran manyan makarantu.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp