Home General Sojojin Nijeriya sun hallaka ‘ƴan ta’adda dubu takwas a Najeriya cikin 2024...

Sojojin Nijeriya sun hallaka ‘ƴan ta’adda dubu takwas a Najeriya cikin 2024 – HDQ

Nigerian Army

Rundunar sojin Najeriya ta ce ta kashe ƴan ta’dda 8,034 daga farko zuwa ƙarshen shekara ta 2024.

Wata sanarwa da darektan yaɗa labarai na rundunar, Manjo-janar Edward Buba ya fitar, ta ce an samu nasarar ne a samame daban-daban da sojoji suka kai yankunan arewa maso gabas da arewa maso yamma da arewa maso tsakiya da kuma sauran yankunan ƙasar.

Ya ce an kama wasu ‘ƴan ta’dda’ 11,263 da kuma ceto mutum 6,376 da aka yi garkuwa da su.

“Mun kuma samu nasarar ƙwato makamai 8,216 da harsasai 211,459. Mun kuma daƙile yunkurin satar ɗanyen mai da kuɗinsa ya kai sama da naira biliyan 57,” in ji Buba.

Sai dai duk da irin waɗannan nasarori da rundunar sojin ke ayyanawa, Najeriya na ci gaba da fama da matsalar tsaro a yankuna daban-daban na ƙasar.

Ko a cikin kwanakin nan an samu ɓullar wata sabuwar ƙungiyar ƴan bindiga arewa maso yammacin Najeriyar, waɗanda ake kira Lakurawa.

Haka nan ma a baya-bayan nan ƙungiyoyin ƴan bindiga sun riƙa dasa nakiyoyi a kan hanyoyin mota a jihar Zamfara, lamarin da ya haifar da asarar rayuka da dukiyoyi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp