Home General Tinubu na son ganin babu wanda ya kwana da yunwa a Najeriya...

Tinubu na son ganin babu wanda ya kwana da yunwa a Najeriya – Minista

Shugaban kasar Bola Tinubu, ya ce samar da abinci shi ne babban abin da gwamnatinsa tafi ba wa muhimmanci.

Karamin ministan noma na kasar, Aliyu Abdullahi, ne ya bayyana hakan inda yace tun bayan da aka rantsar da shugaba Tinubu a watan Mayun 2023, gwamnatinsa ta bullo da shirye-shirye da dama domin tabbatar da an wadata kasar da abinci.

Cikin wata hira da gidan talbijin na Sunrise Daily ya yi da ministan, ya ce a cikin shirye-shirye Tinubu, samar da abinci shi ne kan gaba haka kuma bunkasa aikin noma ma na cikin manyan muradun shugaban kasar saboda baya ga samar da abinci da bangaren noma zai yi zai kuma bunkasa tattalin arzikin kasa.

Aliyu Abdullahi, ya ce shugaba Tinubu, ya damu matuka da matsalar karancin abincin da ake fama da ita a kasa,inda ya ce a wasu lokutan shugaba Tinubun kan sanar da su cewa babban burinsa shi ne ya kai al’ummar Najeriya matsayin da babu wanda zai kwana da yunwa.

Hauhawar farashin kayan abinci da ake fama da ita a Najeriya a baya bayannan, ta jefa miliyoyin mutane cikin yunwa a Najeriya.

A wannan yanayi da ake ciki, gwamnatin tarayyar Najeriya ta bullo da wasu hanyoyi na saukaka rayuwa ciki har da rabon tallafin abinci ga miliyoyin ‘yan Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp