Home General Ƴan ta’adda sama da dubu 129 suka mika wuya ga sojojin Najeriya...

Ƴan ta’adda sama da dubu 129 suka mika wuya ga sojojin Najeriya cikin watanni 6

Babban Hafsan Hafsoshin Sojoin Najeriya, Janar Christopher Musa, ya bayyana cewa ƴan ta’addan Boko Haram 129,417 da iyalansu sun mika wuya ga jami’an tsaro tsakanin ranar 10 ga watan Yuli zuwa 9 ga watan Disamban wannan shekara ta 2024.

Babbabn hafsan rundunar sojin ƙasa na Najeriya ya bayyana haka ne a taron tsaro na Afrika karo na 18 da ke gudana a birnin Doha na ƙasar Qatar.

Taron, mai taken: “Haɓaka tsaro don samar da Zaman Lafiya wanda Mista Patrick Agbambu na ƙungiyar Watch Africa Initiative ya shirya, ya samu halartar masu ruwa da tsaki kan harkokin tsaro daga ƙasashen Najeriya da Guinea Bissau da Gambia da Afirka ta Kudu da Kenya da kuma Qatar.

Janar Musa a jawabinsa ya bayyana cewa alkaluman sun hada da mayaka 30,426, mata 36,774, da yara 62,265.

A cewarsa, wannan nasara ta nuna ci gaban da ake samu wajen samun zaman lafiya a tsakanin al’umma da ke bunkasa zamantakewa da tattalin arziki a Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp