Home General Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kula da gidajen yari

Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kula da gidajen yari

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya naɗa Nwakuche Ndidi, a matsayin shugaban riƙo na hukumar kula da gidajen yarin ƙasar.

Cikin wata sanarwa da sakataren ma’aikatar hukumar tsaro ta sibil difens da hukumar kashe gobara da ta shige da fice, Ja’afaru Ahmed ya ce naɗin Ndidi zai fara aiki daga ranar 15 ga watan Disamba.

Naɗin nasa na zuwa ne bayan ƙarewar wa’adin shugaban hukumar na yanzu, Haliru Nababa.

A ranar 18 ga watan Fabrairu ne dai tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya naɗa Nababa a muƙamin.

An haifi Nwakuche Ndidi ranar 26 ga watan Nuwamban shekarar 1966 a garin Oguta na jihar Imo.

Kafin naɗinsa kan muƙamin shi ne mataimakin shugaban hukumar mai lura da horaswa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp