Home General Tattalin arzikin Najeriya yana haɓaka – Tinubu

Tattalin arzikin Najeriya yana haɓaka – Tinubu

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ce matakan da suka ɗauka na inganta tattalin arzikin ƙasar sun fara haifar da ɗa mai ido.

Tinubu ya bayyana haka ne a cikin jawabin da ya gabatar a majalisar dokoki, inda ya ce, “gyare-gyaren da muka yi sun fara haifar da ɗa mai ido.

“Ƴan Najeriya sun kusa fara cin gajiyar ingantaccen tattalin arziki, Ƙasarmu tana samun ci gaba sosai a fagen tattalin arziki.”

Ya ƙara da cewa tattalin arzikin Najeriya ya inganta, inda a cewarsa ya haɓaka da kashi 3.46 a rubu’i na uku na shekarar 2024, daga kashi 2.54 a rubu’i na uku na shekarar 2023.

Sai dai shugaban majalisar dattawan Najeriya, Godswill Akpabio, ya yi kira ga shugaban ƙasa Bola Tinubu da ya ja kunnen “ministocinsa masu taurin kai” waɗanda ba sa amsa gayyatar majalisar dokoki.

Akpabio ya ce bai kamata irin waɗannan ministocin su samu gurbi a gwamnatinsa ba.

Akpabio ya bayyana haka ne a ranar Laraba, a lokacin da shugaban ƙasar yake gabatar da kasafin kuɗin 2025.

“Waɗanda suke ƙin amsa gayyatar majalisar dokoki ba ƴansiyasa ba ne, don haka bai kamata su samu gurbi a gwamnatinka ba,” kamar yadda Akpabio ya bayyana wa Tinubu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp