Home General CISLAC ta yi gargaɗi kan cushe a kasafin kuɗin 2025

CISLAC ta yi gargaɗi kan cushe a kasafin kuɗin 2025

Cibiyar rajin kyautata ayyukan majalisar dokoki da yaƙi da rashawa a Najeriyar wato CISLAC, ta yi kira da a guji yin cushe a kasafin kuɗin 2025, tare da kira ga gwamnatin tarayya ta tabbatar da kasafta kuɗaɗe kan abubuwan da ƴan ƙasar ke buƙata.

A wata sanarwa da shugaban cibiyar, Auwal Ibrahim Musa (Rafsanjani), ya fitar, CISLAC ta ce cushe a kasafin kuɗi da kasafta kuɗaɗe masu yawa a ayyukan da ba su cancanta ba, bai dace ba, inda ya yi misali da kasafta wa ma’aikatar wasanni da ta Neja Delta kuɗaɗe waɗanda an riga an rufe su.

Da take amfani da rahoton babban mai binciken kuɗi na bana, CISLAC ta bayyana wasu kuɗaɗe da aka cire da suka sha banbam, inda ta ce an cire sama da naira biliyan 197.72 domin wasu ayyuka a ma’aikatu tsakanin 2020 da 2021 ba bisa ƙa’ida ba.

Cibiyar sai ta yi kira ga majalisar da ta yi nazarin kasafin kuɗin cikin mutunci da nagarta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp