Home General Sokoto: Babu hujjar kashe mutanen da babu ruwansu – Atiku

Sokoto: Babu hujjar kashe mutanen da babu ruwansu – Atiku

Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban ƙasa a jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar ya ce babu wata hujjar da za a bayar kan kashe mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba.

Atiku ya bayyana haka a saƙonsa na jaje game da ibtila’in da ya auku a jihar Sokoto, inda hare-haren sojoji ‘bisa kuskure’ ya yi ajalin aƙalla mutum 10, ya jikkata wasu.

Atiku ya ce yadda kuskuren ke maimiatuwa ya sa ake tambayar wane darasi aka ɗauka a baya.

A cewarsa, “A ranar 3 ga Disamban 2023, gomman mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba ne suka rasu a Tudun Biri da ke Kaduna. Shin mutum nawa za su ƙara mutuwa kafin a ɗauki mataki? Duk da cewa yana da kyau a ƙaddamar da hare-hare kan ƴanbindiga, amma ai akwai buƙatar a yi amfani da ƙwarewa.”

“Babu wata hujjar da za a bayar kan kashe mutanen da babu ruwansu. Irin haka na nuna rashin ƙwarewa da tauye haƙƙin ɗan’adam.”

Ya ce hakan zai sa mutane su kasa bambance masu kare su da waɗanda suka kashe, inda ya ce dole a kawo ƙarshen irin wannan kashe-kashen bisa kuskure.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp