Home General Gwamnatin Zamfara ta amince da 70,000 a matsayin sabon albashi mafi ƙanƙanta

Gwamnatin Zamfara ta amince da 70,000 a matsayin sabon albashi mafi ƙanƙanta

Gwamnatin jihar Zamfara ta amince da naira 70,000 a matsayin sabon albashi mafi ƙanƙanta.

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ya ce daga yanzu ma’aikatan jihar za a fara biyan ma’aikatan jihar da sabon tsarin albashin.

Ya kuma ce gwamna Dauda Lawal ya amince da ƙarin albashi ko kuma alawus na ƙarin wata ɗaya ga ma’aikata a faɗin jihar.

“Wannan shi ne irinsa na farko a tarihin Zamfara, wanda kuma gwamna Dauda Lawal ya biya a cikin watan Disamba,” in ji sanarwar.

Kakakin gwamnan ya ce dukkan ma’aikatan jihar, ciki har da waɗanda suka yi ritaya za su samu kashi 30 na alawus.

Gwamnan Dauda Lawal ya ce ya amince da albashi mafi ƙanƙantan da kuma alawus ne domin taimakawa ma’aikatan jihar a wannan lokaci na bukukuwan karshen shekara da kuma ƙara musu karfin gwiwa wajen aiki tukuru wajen kai jihar gaba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp