Home General Gwamnatin Zamfara ta amince da 70,000 a matsayin sabon albashi mafi ƙanƙanta

Gwamnatin Zamfara ta amince da 70,000 a matsayin sabon albashi mafi ƙanƙanta

Gwamnatin jihar Zamfara ta amince da naira 70,000 a matsayin sabon albashi mafi ƙanƙanta.

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ya ce daga yanzu ma’aikatan jihar za a fara biyan ma’aikatan jihar da sabon tsarin albashin.

Ya kuma ce gwamna Dauda Lawal ya amince da ƙarin albashi ko kuma alawus na ƙarin wata ɗaya ga ma’aikata a faɗin jihar.

“Wannan shi ne irinsa na farko a tarihin Zamfara, wanda kuma gwamna Dauda Lawal ya biya a cikin watan Disamba,” in ji sanarwar.

Kakakin gwamnan ya ce dukkan ma’aikatan jihar, ciki har da waɗanda suka yi ritaya za su samu kashi 30 na alawus.

Gwamnan Dauda Lawal ya ce ya amince da albashi mafi ƙanƙantan da kuma alawus ne domin taimakawa ma’aikatan jihar a wannan lokaci na bukukuwan karshen shekara da kuma ƙara musu karfin gwiwa wajen aiki tukuru wajen kai jihar gaba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp