Home General PDP ta zargi ‘yan APC da satar tiriliyan 25

PDP ta zargi ‘yan APC da satar tiriliyan 25

Babbar jam’iyyar adawa a Najeriya ta PDP ta nemi Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya ƙaddamar da bincike kan kuɗaɗe naira tiriliyan 25 da ta zargi ‘yan jam’iyyarsa ta APC da sacewa.

PDP ta yi wannan kira ne a saƙon da ta wallafa na sabuwar shekara, wanda kakakinta na ƙasa Debo Ologuagba ya sanya wa hannu ranar Talata.

“Ya kamata shugaban ƙasa ya wanke kansa game da yaƙi da cin hanci da rashawa ta hanyar ba da umarnin yin bincike da kuma dawo da sama da tiriliyan 25 da aka ce shugabannin APC da jami’an gwamnati sun sace,” in ji sanarwar.

Jam’iyyar ta kuma nemi shugaban ya bayyana adadin kuɗaɗen da gwamnatinsa ta tara daga cire tallafin man fetur da ya yi a watan Mayun 2023.

Haka nan, PDP ta nemi Tinubu ya kawo ƙarshen matsalar tsaro, da yunwa, da kuma ƙarancin man fetur “domin sauƙaƙa wa rayuwar ‘yan Najeriya”.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp