Home AFIRKA Tubabbun mayaƙan Boko Haram 124 za su koma rayuwar fararen hula a...

Tubabbun mayaƙan Boko Haram 124 za su koma rayuwar fararen hula a Nijar

Aƙalla tubabbun mayaƙan Boko Haram 124 ne mahukunta Jamhuriyyar Nijar suka yaye a ƙarshen makon da ya gabata, bayan da aka basu horo na musamman don sauya ɗabi’unsu da nufin ci gaba da rayuwar fararen hula a cikin jama’a.

A ranar Asabar ɗin da ta gabata ne mahukuntan na Nijar suka gudanar da bikin yaye tubabbun mayaƙan na Boko Haram 124 adadin da ya ƙunshi har da ƙananan yara 44 bayan da aka basu horo kan ayyukan dogaro da kai daban-daban.

Gwamnan jihar Diffa da ke kudu maso gabashin ƙasar Janar Mahamadou Ibrahim Bagadoma yayin jawabinsa wajen bikin yaye tubabbun ƴan ta’addan ya ce abin farin ciki ne samun nasarar sauya ɗabi’un mutanen don mayar da su cikin fararen hula don ci gaba da rayuwa kamar kowa.

Wata sanarwa da ma’aikatar cikin gida ta fitar a Jamhuriyyar ta Nijar ta ce dukkanin tubabbun ƴan ta’addan 124 sun samu takardun shaidar kammala samun horo ta yadda ake da yaƙinin za su yi ingantacciyar rayuwa cikin fararen hula.

Wannan ne karon farko da Nijar ke yaye tubabbun mayaƙan Boko Haram tare da mayar da su cikin al’umma ko da ya ke hamɓararren shugaban ƙasar Bazoum Mohammed ya yi makamancin wannan yunƙurin a shekarar 2023 watanni gabanin yi masa juyin mulkin.

Tun shekarar 2017 ne tubabbun mayaƙan fiye da 700 suka ajje makamansu wanda ya bayar da damar fara yi musu horo na musamman don mayar da rayuwarsu da tunaninsu irin na sauran fararen hula.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp