Home General Mun samar wa gwamnatin tarayya naira tiriliyan 10 a 2024 – NNPCL

Mun samar wa gwamnatin tarayya naira tiriliyan 10 a 2024 – NNPCL

Kamfanin man fetur na Najeriya NNPCL ya ce ya zuwa watan Satumban shekarar 2024, kuɗin da ya samar wa gwamnatin tarayya ya kai naira tiriliyan 100.

Shugaban kamfanin, Mele Kyari ne ya sanar da hakan a lokacin da ya bayyana a gaban kwamitin kuɗi na majalisar dattawa, inda yake kare kasafin kuɗin kamfanin na bana.

Ya ce NNPCL na fitar da bayanan asusunsa na shekara-shekara, “Hada-hadarmu a fili suke, kuma muna bayyana duk harkokin kuɗin da muka yi a fili ba tare da nuƙu-nuƙu ba,” in ji shi kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Kyari ya ce kamfanin na NNPCL ne kamfanin da ya fi biyan haraji, kuma wanda ya fi samar da riba ga masu zuba jari.

Sai dai ya ce sai sun zauna tare da daraktocin kamfanin ne za su iya fitar da hasashen kuɗin da za su samar a bana.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp