Home General Bama Bukatar yin siyasa da Kwankwaso – APC kano

Bama Bukatar yin siyasa da Kwankwaso – APC kano

APC

Jam’iyyar APC ta jihar Kano ta ce kokarin shigowa APC Kwankwaso yake yi shi ne Dalilin sa ya Abdulmumin Jibrin Kofa ya fara kiraye-kirayen a sami sulhu tsakanin Kwankwaso da Ganduje.

“Maganar sulhu tsakanin Kwankwaso da Ganduje da Kofa yazo da ita yaudara ce, a siyasance ba ma buƙatar yin siyasa tare da Kwankwaso”.

Mai magana da yawun Jam’iyyar APC reshen jihar Kano Ahmad S Aruwa ne ya bayyana hakan yayin wata ganawa da ya yayi da Hikima Radio dake Kano.

” So suke so dawo APC don su kwace ta daga wajenmu, domin Kwankwaso ya saba yin hakan tun da ya yiwa Malam Ibrahim Shekarau Wanda ta dole sai da muka bar masa APC muka koma PDP, haka kuma ya sake yi mana a PDPn don haka mun gano wayon”. Inji Kakakin APC

Ya ce idan da gaske ke gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ne ya kamata ya dai-data Kwankwaso da Ganduje, amma ba Kofa ba.

” Idan ka lura da yadda Kofa ya tsayyano mukaman da Kwankwaso ya rike da wadanda Ganduje ya rike zaka gane shi (Kofa) ya yi kankanta ya ce zai sulhunta Kwankwaso da Ganduje”. A cewar Aruwa

Kakakin APC reshen jihar Kano ya ce su ba sa bukatar yin sulhu tsakanin Kwankwaso da Ganduje saboda a cewarsa daga karshe cewa za ayi a hade, kuma in an hade su za a cutar.

Idan za a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito Dan majalisar tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Kiru da Bebeji Abdulmumin Jibrin Kofa a karshen makon da muke bankwana da shi , ya ce ya sama wajibi a sulhunta Ganduje da Kwankwaso saboda cigaban jihar Kano

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Abin da Obi ya Fada Kan Atiku - Dele MomoduHukumar EFCC ta Gurfanar da Ma'aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bnFiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a Katsina
X whatsapp