Home General Mun kashe ƴanbindiga ciki har da ɗangidan Bello Turji – Sojoji

Mun kashe ƴanbindiga ciki har da ɗangidan Bello Turji – Sojoji

Dakarun Najeriya da suke aikin soji na musamman Fansan Yamma sun ce sun kashe ƴandinga da dama, ciki har da ɗan cikin Turji a wani samame da suka kai a sansanin ɗanbindigar.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da kakakin hedkwatar taron Najeriya, Edward Buba ya fitar, inda ya ce, “a ranar 17 ga Janairu, dakarun Fansan Yamma sun kutsa dazukan da ke yankin Shinkafi da Kagara da Fakai da Moriki da Maiwa da Chindo, inda suka kashe gomman ƴanbindiga, sannan suka kashe ɗan cikin Bello Turji a Fakai, inda yake ɓoyewa.”

Sanarwar ta ƙara da cewa sojojin sun samu ƙashe ƴanbindiga da dama, da ɓarnata ma’ajiyarsu, “sannan sun ceto wasu waɗanda Bello Turji ya yi garkuwa da su, bayan ya tsere.”

Sanarta ta ce sojojin sun kai wani samamen a sansanin wani ɗanbindigar mai suna Idi Mallam, “inda sojoji suka kashe ƴanbindiga 3, da kama mutum 3 da ake zargi da taimakon ƴanbindiga, tare da ƙwato wasu makamai da dabbobin da suka sace.”

A ƙarshe Buba ya ce sojojin za su cigaba da fatattarkar ƴanbindigar a ƙoƙarinsu na tabbatar da zaman lafiya a faɗin ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp