Home General Alamu na nuna yiwuwar Najeriya za ta ga ƙarancin mahajjata a bana

Alamu na nuna yiwuwar Najeriya za ta ga ƙarancin mahajjata a bana

Alƙaluma na nuna yiwuwar Najeriya ta fuskanci ƙarancin maniyyata a hajjin bana, wanda ke da nasaba da hauhawar farashin kujerar hajjin bisa bayanan da hukumar kula da aikin hajji ta ƙasar NAHCON ta fitar a rana Litinin.

Hankula sun tashi matuƙa bayan da hukumar aikin hajjin Najeriyar ta fitar da farashin kujerar ta bana wanda ya tasamma miliyan 8 da rabi a wasu yankunan har ya zarta hakan.

Dai dai lokacin da ya rage ƙasa da wata guda kan wa’adin da NAHCON ta bayar wajen kammala biyan kudin aikin hajjin na bana, har yanzu ana ganin ƙarancin mutanen da ke miƙa kuɗinsu don sayen kujerun aikin hajjin na bana wanda alƙaluman ke nuna yiwuwar ya iya zama hajji mafi ƙarancin jama’a daga Najeriyar.

Alƙaluman farashin da NAHCON ta fitar ya nuna cewa mahajjata daga kudancin ƙasar za su biya tsabar kudi har naira miliyan 8 da dubu 700 yayinda maniyyata da arewa maso gabashin Najeriya kuma za su biya naira miliyan 8 da dubu 300 a gefe guda mahajjata daga arewaci kuma za su biya naira miliyan 8 da dubu 400.

Shugaban hukumar ta NAHCON farfesa Abdullahi Saleh Usman ya bayyana cewa hukumar ta yi aiki tuƙuru wajen ganin farashin hajjin a bana bai kai naira miliyan 9 ba.

A baya dai an yi fargabar farashin aikin hajjin a bana ya iya kai naira miliyan 10 musamman lura da karyewar darajar takardar kudi ta Najeriyar naira.

Ƙarƙashin dokokin hukumar NAHCON dai dukkanin maniyyacin da ya gaza biyan adadin kudin aikin hajjin kafin nan da ranar 5 ga watan Fabarairu kai tsaye sai dai ya jira zuwa shekara mai zuwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Samar da Tsaro: Sojojin Najeriya sun Kama ƴan ƙasashen Wajen 46Ta'addanci: Za a Gurfanar da Mutane 400 a Gaban Kotun Tarayya da ke AbujaAn Ceto Matar Janar Rabe da ya Rasu a Hannun ƴan BindigaHauhawar Farashin Kayan Masarufi a Najeriya ya ƙaru Zuwa Kashi 15.93Rundunar Sojin Najeriya ta Gudanar da Hare-Hare Kan Maɓoyar ƴan Bindiga a Jihar KatsinaZaben 2027: NDC ta Tsayar da Ɗan Kwankwaso Mataimakin ɗan Takarar Gwamnan KanoKotu ta Umarci INEC da ta Soke Rajistar ADC Tare da Jam’iyyu 4Manyan Tsofaffin Jami'an Soji 10 da Suka Rasa Rayukansu a Hannun ƴan Ta'addaTarihin Rayuwar Janar Rabe da ya Rasu a Hannun ƴan BindigaMatsalar Tsaro: Masu Zanga-Zanga Sun Tare Babbar Hanyar AbujaDuk Wanda aka Kama Yana Kasuwanci da 'Yan Ta'adda, za a ɗauke shi a Matsayin ɗan ta’adda - Christopher MusaFarashin ɗanyen Mai ya Faɗi Bayan Amurka ta Soke Sabbin Hare-Haren kaiwa IranAmurka ta yi sulhu kan yaƙin da ta ke yi da Iran - TrumpMajalisar Wakilan Najeriya ta Amince da ƙudirin Dokar Kafa ’Yan sandan JihaHukuncin da aka Yanke wa Masu Alaƙa da Sace ɗaliban Jihar Neja
X whatsapp