Home General Alamu na nuna yiwuwar Najeriya za ta ga ƙarancin mahajjata a bana

Alamu na nuna yiwuwar Najeriya za ta ga ƙarancin mahajjata a bana

Alƙaluma na nuna yiwuwar Najeriya ta fuskanci ƙarancin maniyyata a hajjin bana, wanda ke da nasaba da hauhawar farashin kujerar hajjin bisa bayanan da hukumar kula da aikin hajji ta ƙasar NAHCON ta fitar a rana Litinin.

Hankula sun tashi matuƙa bayan da hukumar aikin hajjin Najeriyar ta fitar da farashin kujerar ta bana wanda ya tasamma miliyan 8 da rabi a wasu yankunan har ya zarta hakan.

Dai dai lokacin da ya rage ƙasa da wata guda kan wa’adin da NAHCON ta bayar wajen kammala biyan kudin aikin hajjin na bana, har yanzu ana ganin ƙarancin mutanen da ke miƙa kuɗinsu don sayen kujerun aikin hajjin na bana wanda alƙaluman ke nuna yiwuwar ya iya zama hajji mafi ƙarancin jama’a daga Najeriyar.

Alƙaluman farashin da NAHCON ta fitar ya nuna cewa mahajjata daga kudancin ƙasar za su biya tsabar kudi har naira miliyan 8 da dubu 700 yayinda maniyyata da arewa maso gabashin Najeriya kuma za su biya naira miliyan 8 da dubu 300 a gefe guda mahajjata daga arewaci kuma za su biya naira miliyan 8 da dubu 400.

Shugaban hukumar ta NAHCON farfesa Abdullahi Saleh Usman ya bayyana cewa hukumar ta yi aiki tuƙuru wajen ganin farashin hajjin a bana bai kai naira miliyan 9 ba.

A baya dai an yi fargabar farashin aikin hajjin a bana ya iya kai naira miliyan 10 musamman lura da karyewar darajar takardar kudi ta Najeriyar naira.

Ƙarƙashin dokokin hukumar NAHCON dai dukkanin maniyyacin da ya gaza biyan adadin kudin aikin hajjin kafin nan da ranar 5 ga watan Fabarairu kai tsaye sai dai ya jira zuwa shekara mai zuwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp