Home General Sojoji sun kashe Aminu Kanawa mataimakin Bello Turji

Sojoji sun kashe Aminu Kanawa mataimakin Bello Turji

Sojoji Najeriya da ke yaƙi da ƴanbindiga a arewa maso yammacin Najeriya sun ce sun kashe wani babban mataimakin gawurtaccen ɗanbindigar nan da ke addabar yankin, Bello Turji, mai suna Aminu Kanawa.

A wata sanarwa da sojojin suka fitar ta ce dakarun dai “sun samu nasarar kashe Aminu Kanawa ne lokacin wani samame da suka kai a duwatsun Fakai da ke ƙaramar hukumar Shinkafi.”

“Ɗanbindigar ya yi ƙaurin suna ne wajen addabar al’ummar ƙananan hukumomin jihar ta Zamfara da ma Sokoto da suka haɗa da Zurmi, Shinkafi, Isa da Sabon Birni.”

Sanarwar ta ƙara da cewa baya ga Aminu Kanawa da suka kashe, sojojin sun jikkata ƴanbindiga irin su Dosso wanda ƙanen Turji ne da kuma Danbokolo wanda shi ma makusancinsa ne.

Har wayau, sanarwar ta ƙara da cewa a wani sabon harin da dakarun suka kai sun samu nasarar kashe manyan kwamandojin Bello Turji kamar haka:

  • Abu Dan Shehu
  • Jabbi Dogo
  • Dan Kane
  • Basiru Yellow
  • Kabiru Gebe
  • Bello Buba
  • Dan Inna Kahon-Saniya-Yafi-Bahaushe,

Rundunar sojojin kamar yadda sanarwar ta ce ta samu damar kashe ƙarin kwamandojin Turji guda 24 da ke ƙoƙarin tserewa daga sansanin Turjin da ke Geɓe da Isa.

Sanarwar ta kuma ce dakarun sun kuma kashe wani ɗanbindiga wanda makusancin Halilu Sububu ne yayin kai farmaki a maɓoyar Bello Turjin, mai suna Suleiman.

Daga ƙarshe sanarwar ta ce samun nasarar kashe ƴanbindigar waɗanda ƙasurgumai ne babban rashi ne ga Bello Turji wanda “nan gaba kaɗan zai zama cikin komarmu”.

Kafar watsa labarai ta PR Nigeria ta wallafa cewa wata majiya daga hedkwatar tsaro ta Najeriya ta tabbatar mata da tserewar Turji zuwa yankin Maradun, sannan mutanen yankin sun tabbatar da ganin wasu babura suna zarya, waɗanda ake tunanin sun ɗauki ƴanbindiga da aka harba ne suna tafiya da su zuwa yankin Kadanya da Bayan Ruwa.

Ko a ranar Talata sai da sojojin suka bayar da sanarwar kashe ɗangidan Bello Turji yayin wani samame da suka kai sansanin ɗanbindigar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Manyan Tsofaffin Jami'an Soji 10 da Suka Rasa Rayukansu a Hannun ƴan Ta'addaTarihin Rayuwar Janar Rabe da ya Rasu a Hannun ƴan BindigaMatsalar Tsaro: Masu Zanga-Zanga Sun Tare Babbar Hanyar AbujaDuk Wanda aka Kama Yana Kasuwanci da 'Yan Ta'adda, za a ɗauke shi a Matsayin ɗan ta’adda - Christopher MusaFarashin ɗanyen Mai ya Faɗi Bayan Amurka ta Soke Sabbin Hare-Haren kaiwa IranAmurka ta yi sulhu kan yaƙin da ta ke yi da Iran - TrumpMajalisar Wakilan Najeriya ta Amince da ƙudirin Dokar Kafa ’Yan sandan JihaHukuncin da aka Yanke wa Masu Alaƙa da Sace ɗaliban Jihar NejaMiyagun ƙwayoyi da Makamai: Jami'an Tsaro Sun Kama Mutane 8 a Jihar YobeAbin da Obi ya Fada Kan Atiku - Dele MomoduHukumar EFCC ta Gurfanar da Ma'aurata Kan Damfarar Kudi Kusan N2bnFiye da Kashi 60 na 'Yan Najeriya a Yanzu Suna Rayuwa Cikiin Fatara - IMFGwamnatin Najeriya ta Caccaki Afrika ta Kudu kan Harin da ake yi wa ƴan ƙasartaƳan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a Sokoto
X whatsapp