Home General Sojoji sun kashe Aminu Kanawa mataimakin Bello Turji

Sojoji sun kashe Aminu Kanawa mataimakin Bello Turji

Sojoji Najeriya da ke yaƙi da ƴanbindiga a arewa maso yammacin Najeriya sun ce sun kashe wani babban mataimakin gawurtaccen ɗanbindigar nan da ke addabar yankin, Bello Turji, mai suna Aminu Kanawa.

A wata sanarwa da sojojin suka fitar ta ce dakarun dai “sun samu nasarar kashe Aminu Kanawa ne lokacin wani samame da suka kai a duwatsun Fakai da ke ƙaramar hukumar Shinkafi.”

“Ɗanbindigar ya yi ƙaurin suna ne wajen addabar al’ummar ƙananan hukumomin jihar ta Zamfara da ma Sokoto da suka haɗa da Zurmi, Shinkafi, Isa da Sabon Birni.”

Sanarwar ta ƙara da cewa baya ga Aminu Kanawa da suka kashe, sojojin sun jikkata ƴanbindiga irin su Dosso wanda ƙanen Turji ne da kuma Danbokolo wanda shi ma makusancinsa ne.

Har wayau, sanarwar ta ƙara da cewa a wani sabon harin da dakarun suka kai sun samu nasarar kashe manyan kwamandojin Bello Turji kamar haka:

  • Abu Dan Shehu
  • Jabbi Dogo
  • Dan Kane
  • Basiru Yellow
  • Kabiru Gebe
  • Bello Buba
  • Dan Inna Kahon-Saniya-Yafi-Bahaushe,

Rundunar sojojin kamar yadda sanarwar ta ce ta samu damar kashe ƙarin kwamandojin Turji guda 24 da ke ƙoƙarin tserewa daga sansanin Turjin da ke Geɓe da Isa.

Sanarwar ta kuma ce dakarun sun kuma kashe wani ɗanbindiga wanda makusancin Halilu Sububu ne yayin kai farmaki a maɓoyar Bello Turjin, mai suna Suleiman.

Daga ƙarshe sanarwar ta ce samun nasarar kashe ƴanbindigar waɗanda ƙasurgumai ne babban rashi ne ga Bello Turji wanda “nan gaba kaɗan zai zama cikin komarmu”.

Kafar watsa labarai ta PR Nigeria ta wallafa cewa wata majiya daga hedkwatar tsaro ta Najeriya ta tabbatar mata da tserewar Turji zuwa yankin Maradun, sannan mutanen yankin sun tabbatar da ganin wasu babura suna zarya, waɗanda ake tunanin sun ɗauki ƴanbindiga da aka harba ne suna tafiya da su zuwa yankin Kadanya da Bayan Ruwa.

Ko a ranar Talata sai da sojojin suka bayar da sanarwar kashe ɗangidan Bello Turji yayin wani samame da suka kai sansanin ɗanbindigar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp